Connect with us

Labarai

SON Ta Bada Shaidar Ingancin Kayayyaki Ga Wasu Kamfanoni A Kaduna

Published

on

Hukumar Kula da Ingancin Kayayyaki ta Najeriya (SON) ta gudanar da bikin bayar da takardun shaidar MANCAP ga kayayyaki 31 da suka cika sharuddan inganci a ofishinta da ke Kaduna.

Taron wata babbar nasara ce ga masana’antun da abin ya shafa, duba da yadda ya kara jaddada muhimmancin tabbatar da inganci a masana’antun cikin gida na Najeriya.

A jawabin maraba da ya gabatar, Injiniya Mamza Irimiya, mai kula da ofishin SON na jihar Kaduna, ya yabawa kokarin wadanda suka sami shaidar, yana mai cewa “Samuwa ko mallakar takardar shaidar MANCAP ba abu ba ne da ake siya, tsari ne na jajircewa da kokari. Yau an karrama ku ne saboda kokarin ku, wanda hakan mataki ne farko , domin tabbatar da ingancin kayyaki abu ne da za a ci gaba da yi lokaci bayan lokaci.”

Injiniya Irimiya ya jaddada muhimmancin kirkire-kirkire da sabbin fasahohi, tare da karfafa gwiwar wadanda suka samu shaidar da su ci gaba da yin kokarin da zai kai kayayyakin su zuwa kasuwannin duniya a maimakon cikin gida kawai.

Ya bayyana cewa, shaidar tana kara wa masu amfani da kayayyakin cikin gida kwarin gwiwa kan ingancin kayayyakin Najeriya.

Wakilin Babban Daraktan SON, Dr. Ifeanyi Chukwunonso Okeke, wato Daraktan Yankin Arewa maso Yamma, Mr. Isaac Omebije Onojo, ya bayyana cewa “Bin ka’idoji a masana’antu yana da matukar muhimmanci, domin rashin yin hakan na iya jefa kasuwancin cikin barazana.Shirin MANCAP yana tabbatar da cewa kayayyakin da ake sarrafawa a Najeriya suna da inganci da aminci ga masu amfani.”

Mr. Onojo ya taya wadanda suka samu shaidar murna, yana kuma karfafa su da su ci gaba da inganta ayyukansu. Ya kuma gargadi masu masana’antu kan illar samar da kayayyaki marasa inganci, yana mai cewa hakan ba wai kawai yana cutar da masu amfani ba ne, har ma yana bata sunan masana’antun.

Ya kara da cewa, “Bin ka’idoji yana bunkasa kasuwanci tare da kare lafiyar jama’a.”

A nasa jawabin, Kwamishinan Harkokin Kasuwanci, Kirkire-Kirkire da Fasaha na jihar Kaduna ya bayyana cewa samun shaidar nan ya nuna jajircewar kamfanonin wajen kare hakkin masu amfani da tabbatar da ingancin kayayyaki.

Ya yaba wa SON bisa kokarin da suke yi wajen tabbatar da cewa kamfanoni da dama sun samu takardun shaidar domin inganta kayayyakin da ke kasuwa.

 

Daga cikin kamfanonin da suka samu takardar MANCAP akwai Global Care Industry Ltd., Simalox Paint and Decoration Services, Matrix Fertilizer Ltd., Euro Form, da Al-babello Trading Company Ltd., da sauransu.

Wannan nasara na da matukar muhimmanci wajen habbaka masana’antu da gamsar da bukatun kasuwa tare da taimakawa ci gaban tattalin arzikin jihar Kaduna.

Shamsuddeen Mannir Atiku

Labarai

Labarai19 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi20 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai20 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara