Labarai
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Kayan Abinci Ga Al’ummar Najeriya
Gwamnatin Tarayya ta ce za ta fara raba hatsi a faɗin ƙasar a wani mataki na rage matsin rayuwa da ƴan Najeriya suke ciki.
Ministan aikin gona Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a yau Litinin a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.
“Ina bai wa ƴan Najeriya da suke cikin halin matsin rayuwa haƙuri. Na san halin ƙunci da ake ciki, musamman ganin fasa rumbunan abinci da kuma wawaso da ake yi,” in ji ministan.
Ya ce yana son ya tabbatarwa ƴan Najeriya cewa gwamnati na ci gaba da ƙoƙari na ganin abubuwa sun daidaita.
Sanata Kyari ya ce shugaban ƙasa ya amince a fara raba Hatsi da ya kai tan dubu arba’in da biyu a faɗin jihohi 36 na ƙasar a wannan mako.
“Muna aiki kafada da kafada da hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA da kuma jami’an tsaro na farin kaya DSS don tabbatar da cewa Hatsin ya kai hannun wadanda suka cancanta, wato mabukata”.
Ministan ya ƙara da cewa za a fitar da tan dubu hamsin da takwas da dari biyar na shinkafa zuwa kasuwanni a cikin farashi mai rahusa.
Har ila yau, ministan ya buƙaci ‘ƴan Najeriya da su ci gaba da mara wa gwamnatin shugaba Bola Tinubu a kokari da take yi na ganin ta shawo kan matsalolin da ƙasar ke fuskanta.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
