Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Kayan Abinci Ga Al’ummar Najeriya

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta ce za ta fara raba hatsi a faɗin ƙasar a wani mataki na rage matsin rayuwa da ƴan Najeriya suke ciki.

Ministan aikin gona Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a yau Litinin a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

Ina bai wa ƴan Najeriya da suke cikin halin matsin rayuwa haƙuri. Na san halin ƙunci da ake ciki, musamman ganin fasa rumbunan abinci da kuma wawaso da ake yi,” in ji ministan.

Ya ce yana son ya tabbatarwa ƴan Najeriya cewa gwamnati na ci gaba da ƙoƙari na ganin abubuwa sun daidaita.

Sanata Kyari ya ce shugaban ƙasa ya amince a fara raba Hatsi da ya kai tan dubu arba’in da biyu a faɗin jihohi 36 na ƙasar a wannan mako.

Muna aiki kafada da kafada da hukumar  bada agajin gaggawa ta kasa NEMA da kuma jami’an tsaro na farin kaya DSS don tabbatar da cewa Hatsin ya kai hannun wadanda suka cancanta,  wato mabukata”.

Ministan ya ƙara da cewa za a fitar da tan dubu hamsin da takwas da dari biyar  na shinkafa zuwa kasuwanni a cikin farashi mai rahusa.

Har ila yau, ministan ya buƙaci ‘ƴan Najeriya da su ci gaba da mara wa gwamnatin shugaba Bola Tinubu a kokari da take yi na ganin ta shawo kan matsalolin da ƙasar ke fuskanta.

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara