Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Bukaci Maniyyata Su Rika Halartar Taron Bita

Published

on

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta yi kira ga maniyyatan jihar  da su halarci taron bita na mako-mako da ake gudanarwa a cibiyoyin da aka kebe a fadin jihar.

Babban Daraktan Hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya yi wannan kiran a Dutse babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa kiran ya zama wajibi domin a horar da Maniyyatan  rukunai da manyan ka’idojin aikin Hajji kamar yadda addinin  ya koyar.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce wajibi ne kowane Maniyyaci ya samu halartar  kashi 80 cikin 100 na taron bitar kafin jigilar su zuwa Saudiyya.

Ya yi nuni da cewa hukumar ta samar da matsuguni tsaftatacce ga maniyyatan jihar a kusa da Harami, inda ya kara da cewa, an kuma kara samar da tsare tsare kan yadda za a ciyar da Alhazan yayin aikin Hajjin.

Don haka ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa tallafin da yake bai wa hukumar domin gudanar da aikin Hajjin na bana.

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai2 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai2 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai2 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi2 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai3 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai3 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai4 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai4 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai4 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara