Labarai
Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Bukaci Maniyyata Su Rika Halartar Taron Bita
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta yi kira ga maniyyatan jihar da su halarci taron bita na mako-mako da ake gudanarwa a cibiyoyin da aka kebe a fadin jihar.
Babban Daraktan Hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya yi wannan kiran a Dutse babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa kiran ya zama wajibi domin a horar da Maniyyatan rukunai da manyan ka’idojin aikin Hajji kamar yadda addinin ya koyar.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce wajibi ne kowane Maniyyaci ya samu halartar kashi 80 cikin 100 na taron bitar kafin jigilar su zuwa Saudiyya.
Ya yi nuni da cewa hukumar ta samar da matsuguni tsaftatacce ga maniyyatan jihar a kusa da Harami, inda ya kara da cewa, an kuma kara samar da tsare tsare kan yadda za a ciyar da Alhazan yayin aikin Hajjin.
Don haka ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa tallafin da yake bai wa hukumar domin gudanar da aikin Hajjin na bana.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai4 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai2 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai4 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana