Labarai
Shugaban Majalisar Musulmi Ya Yi Kakkausar Suka Game Da Yadda Wasu Malamai Ke Sukar Junansu
Shugaban Majalisar Musulmi ta Kasa Ustaz Sadiq Abdulrahman Abiodun ya tunatar da malaman addinin musulunci bukatar yin amfani da hikima da kyautatawa yayin gabatar da wa’azi akan ka’idojin shari’ar musulunci domin sanya mabiyan su akan turbar da ta dace.
Shugaban ya sanar da hakan ne a taron bita ta yini guda da aka shiryawa malamai da limamam addinin musulunci a Kaduna.
Ustaz Sadiq Abdulrahman Abiodun ya nuna rashin jin dadin sa bisa yadda wasu malaman addinin musulunci ke amfani da kafafen sada zumunta na zamani suna sukar junan su, wanda a cewar sa wannan bai dace da tsarin addinin musulunci ba, maimakon haka su yi amfani da kafafen wajen yada addinin musulunci.
Shugaban ya ce ya zama wajibi ga Majalisar Kula da Addinin Musulunci ta Kasa ta janyo hankalin malamai su shiga taitayinsu, a matsayinsu na masu dora mutane akan tafarkin bautawa Mahalicci sannan su gudanar da tsaftatacciyar rayuwa.
Ya yi kira ga iyaye musulmi su rika duba takardu da darussan da ake koyawa ‘ya’yansu a makarantu don gudun ka da a koya musu munanan dabi’u da ka iya bata musu tarbiya.
Da yake gabatar da makala akan muhimmancin ilimi ga rayuwar malaman addinin musulunci, limamin masallacin MCAN a Kabala da Unguwan Mu’azu, Alfa Abdulrasheed Muhammed Jami’u Al-Iraqi, ya ce ya zama wajibi malaman addinin musulunci su zurfafa neman ilimin addini domin ilmantar da mabiya dokokin shari’ar musulunci sau da kafa a kasar nan.
Ya shawarce su da kada su nuna son rai da jahiltar fannin da basu da kwarewa akai, don gudun kada su yada karya akan addinin musulunci, wanda yin hakan ka iya batar da mutane.
Shi ma a makalar da ya gabatar mai taken, Dabarun Gabatar da Wa’azi, wanda malamai ya kamata su rika amfani da su, Alfa Ahmed Busairy ya ce ya zama wajibi malaman addinin musulunci su lakanci ilimin nahawu, baya ga sanin Qur’ani da Sunnah.
Ya kara da cewa, akwai bukatar malaman addinin musulunci su yi amfani da hikima da nuna juriya da hakuri yayin gabatar da wa’azi, kasancewar suna mu’amula da mutane masu sabanin fahimta.
Taron bitar na yini guda ya samu halartar malami da Limaman addinin musulunci daga kungiyoyin musulunci da dama.
Shamsuddeen Munir Atiku
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United