Connect with us

Labarai

Shugaban Majalisar Musulmi Ya Yi Kakkausar Suka Game Da Yadda Wasu Malamai Ke Sukar Junansu

Published

on

 

Shugaban Majalisar Musulmi ta Kasa Ustaz Sadiq Abdulrahman Abiodun ya tunatar da malaman addinin musulunci bukatar yin amfani da hikima da kyautatawa yayin gabatar da wa’azi akan ka’idojin shari’ar musulunci domin sanya mabiyan su akan turbar da ta dace.

Shugaban  ya sanar da hakan ne a taron bita ta yini guda da aka shiryawa malamai da limamam addinin musulunci a Kaduna.

Ustaz Sadiq Abdulrahman Abiodun ya nuna rashin jin dadin sa bisa yadda wasu malaman addinin musulunci ke amfani da kafafen sada zumunta na zamani suna sukar junan su, wanda a cewar sa wannan bai dace da tsarin addinin musulunci ba, maimakon haka su yi amfani da kafafen wajen yada addinin musulunci.

Shugaban ya ce ya zama wajibi ga Majalisar Kula da Addinin Musulunci ta Kasa ta janyo hankalin malamai su shiga taitayinsu, a matsayinsu na masu dora mutane akan tafarkin bautawa Mahalicci sannan su gudanar da tsaftatacciyar rayuwa.

Ya yi kira ga iyaye musulmi su rika duba takardu da darussan da ake koyawa ‘ya’yansu a makarantu don gudun ka da a koya musu munanan dabi’u da ka iya bata musu tarbiya.

Da yake gabatar da makala akan muhimmancin ilimi ga rayuwar malaman addinin musulunci, limamin masallacin MCAN a Kabala da Unguwan Mu’azu, Alfa Abdulrasheed Muhammed Jami’u Al-Iraqi, ya ce ya zama wajibi malaman addinin musulunci su zurfafa neman ilimin addini domin ilmantar da mabiya dokokin shari’ar musulunci sau da kafa a kasar nan.

Ya shawarce su da kada su nuna son rai da jahiltar fannin da basu da kwarewa akai, don gudun kada su yada karya akan addinin musulunci, wanda yin hakan ka iya batar da mutane.

Shi ma a makalar da ya gabatar mai taken, Dabarun Gabatar da Wa’azi, wanda malamai ya kamata su rika amfani da su, Alfa Ahmed Busairy ya ce ya zama wajibi malaman addinin musulunci su lakanci ilimin nahawu, baya ga sanin Qur’ani da Sunnah.

Ya kara da cewa, akwai bukatar malaman addinin musulunci su yi amfani da hikima da nuna juriya da hakuri yayin gabatar da wa’azi, kasancewar suna mu’amula da mutane masu sabanin fahimta.

Taron bitar na yini guda ya samu halartar malami da Limaman addinin musulunci daga kungiyoyin musulunci da dama.

Shamsuddeen Munir Atiku

Labarai

Labarai20 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi20 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai20 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara