Connect with us

Labarai

Shugaban Majalisar Musulmi Ya Yi Kakkausar Suka Game Da Yadda Wasu Malamai Ke Sukar Junansu

Published

on

 

Shugaban Majalisar Musulmi ta Kasa Ustaz Sadiq Abdulrahman Abiodun ya tunatar da malaman addinin musulunci bukatar yin amfani da hikima da kyautatawa yayin gabatar da wa’azi akan ka’idojin shari’ar musulunci domin sanya mabiyan su akan turbar da ta dace.

Shugaban  ya sanar da hakan ne a taron bita ta yini guda da aka shiryawa malamai da limamam addinin musulunci a Kaduna.

Ustaz Sadiq Abdulrahman Abiodun ya nuna rashin jin dadin sa bisa yadda wasu malaman addinin musulunci ke amfani da kafafen sada zumunta na zamani suna sukar junan su, wanda a cewar sa wannan bai dace da tsarin addinin musulunci ba, maimakon haka su yi amfani da kafafen wajen yada addinin musulunci.

Shugaban ya ce ya zama wajibi ga Majalisar Kula da Addinin Musulunci ta Kasa ta janyo hankalin malamai su shiga taitayinsu, a matsayinsu na masu dora mutane akan tafarkin bautawa Mahalicci sannan su gudanar da tsaftatacciyar rayuwa.

Ya yi kira ga iyaye musulmi su rika duba takardu da darussan da ake koyawa ‘ya’yansu a makarantu don gudun ka da a koya musu munanan dabi’u da ka iya bata musu tarbiya.

Da yake gabatar da makala akan muhimmancin ilimi ga rayuwar malaman addinin musulunci, limamin masallacin MCAN a Kabala da Unguwan Mu’azu, Alfa Abdulrasheed Muhammed Jami’u Al-Iraqi, ya ce ya zama wajibi malaman addinin musulunci su zurfafa neman ilimin addini domin ilmantar da mabiya dokokin shari’ar musulunci sau da kafa a kasar nan.

Ya shawarce su da kada su nuna son rai da jahiltar fannin da basu da kwarewa akai, don gudun kada su yada karya akan addinin musulunci, wanda yin hakan ka iya batar da mutane.

Shi ma a makalar da ya gabatar mai taken, Dabarun Gabatar da Wa’azi, wanda malamai ya kamata su rika amfani da su, Alfa Ahmed Busairy ya ce ya zama wajibi malaman addinin musulunci su lakanci ilimin nahawu, baya ga sanin Qur’ani da Sunnah.

Ya kara da cewa, akwai bukatar malaman addinin musulunci su yi amfani da hikima da nuna juriya da hakuri yayin gabatar da wa’azi, kasancewar suna mu’amula da mutane masu sabanin fahimta.

Taron bitar na yini guda ya samu halartar malami da Limaman addinin musulunci daga kungiyoyin musulunci da dama.

Shamsuddeen Munir Atiku

Labarai

Fasaha1 hour ago

Gwamnan Kaduna Ya Kaddamar Da Sabbin Ajujuwa A Zaria

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya kaddamar da rukunin ajujuwa 18 a makarantun Basic Education guda biyu dake karamar hukumar...

Fasaha1 hour ago

Shugaban Kasa Ya Kaddamar Sabon Birnin Kasuwanci A Abuja

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da samarda wani da za a samar don gudanarda harkokin kasuwanci a cikinsa da...

Labarai2 hours ago

Kungiyar CAN Ta Rasa Mata Shida A Hadarin Mota A Taraba

An bayyana cewa wasu ’yan kungiyar mata ta kungiyar Kiristoci ta Najeriya (WOWICAN) su shida ne suka rasa rayukansu a...

Labarai2 hours ago

‘Yan Sakai Jihar Taraba Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Yi Garkuwa

Rundunar ‘yan banga ta Najeriya (VGN) reshen jihar Taraba ta yi nasarar ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa...

Ilimi2 hours ago

Talatar Nan Jirgin farko na Maniyatan jihar Kwara Zai Tashi

An dage tashin jirgin farko daga filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon na kasa da kasa na Ilorin don...

Labarai3 hours ago

HARIN MASALLACIN KANO: Obi Ya Ziyarci Wadanda suka Mutu

  Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya ziyarci wadanda kona masallacin Kano...

Labarai3 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi Ta Yi Kiran A Yiwa Mijinta Addu’a

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce addu’a ita ce ginshikin duk wani shugabanci mai nasara, don...

Labarai3 hours ago

Gwamnatin Kano Ta Rufe Asibitin Kwanar Ganduje A Kano

Gwamnatin jihar Kano, ta rufe tare asibitin Kwanar Ganduje dake unguwar Sharada Karamar Hukumar Kano Municipal.   Babban daraktan hukumar...

Labarai3 hours ago

Shugaban Iran Ebrahim Raisi Ya Rasu A Hatsarin Jirgi

Jami’an Iran sun ce Shugaba Ebrahim Raisi da ministan harkokin wajen ƙasar, Hossein Amir-Abdollahian sun rasu a wani hatsarin jirgin...

Labarai14 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Mafi Shahara