Labarai
Tinubu Ya Kaddamar Da Layin Dogo Na Zamani A Legas
Shugaban Kasar Najeriya, Bola Tinubu, ya kaddamar da layin dogo ‘Red line’ na zamani a birnin Legas.
Aikin mai tsawon kilomita 37 zai karade wasu manyan yankunan birnin, wanda shi ne cibiyar kasuwancin kasar.
A kullum za’a dinga jigilar akalla fasinjoji kusan dubu dari biyar (500,000), a tsakanin Agege da Oshodi da Ikeja da Mushin da Yaba zuwa Oyingbo.
Da yake jawabi yayin kaddamar da tsarin sifurin na Red line, shugaba Tinubu ya sake jaddada kudurin gwamnatinsa na inganta abubuwan more rayuwa a kasar.
Tinubu ya yi hasashen cewa, layin dogo zai kawo babbar dama ga tattalin arzikin jihar, yana mai nuna godiya ga hukumar LAMATA da abokan huldar da suka tabbatar da kammala kashi na farko na aikin.
Shugaban kasar ya ce babu gudu, ba ja da baya dangane da sauye-sauyen da gwamnatinsa ta kudiri aniyar aiwatarwa.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United