Connect with us

Labarai

Gwamnatin Neja Ta Haramtawa Motocin Da Suka Fito Daga Hanyar Maje Bin Gadar Dikko

Published

on

Gwamnatin Jihar Neja ta ba da umarnin hana motocin da suka  fito daga Maje hawa gadar Dikko.

Gwamnan jihar Mohammed Umar Bago ya ba da umarnin a lokacin da ya ziyarci wurin da wata tankar mai  ta yi  gobara a mahadar Dikko da ke karamar hukumar Gurara ta jihar Neja.

Gwamnan, wanda ya koka kan yadda wasu direbobi ke nuna halin ko-in-kula yayin tuki, ya ce ba a amince duk wata mota da ta fito daga Maje ta bi ta gadar Dikko ba, sai dai su bi karkashin gadar zagayo kan hanyarsu.

Ya kuma umurci babban kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta tarayya da ya kafa rundunar tsaro a yankin domin tabbatar da aiwatar da wannan umarni, yayin da ya yi kira ga kungiyoyin sufuri da abin ya shafa da su ba hukumar kiyaye hadurra ta kasa hadin kai.

Sai dai Gwamnan ya bayyana fashewar tankar mai da ta yi sanadin mutuwar mutane da dama a matsayin abin tausayi tare da gode wa Allah da lamarin bai kai ga al’ummar da ke makwabtaka da su ba.

Umar Bago ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta daukar matakin kammala aikin titin Minna zuwa Suleja domin jinkirin aikin hanyar yana haddasa asarar  rayuka da dukiyoyi.

Gwamnan ya godewa Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, da Hukumar Kashe Gobara, da Hukumar kiyaye hadurra ta kasa, da Kungiyar Sufuri ta Kasa (NURT) da sauran hukumomin da suka bayar da gudunmawa wajen kawo dauki ga  wadanda fashewartankarya rutsa da su.

Ya ce za a kara  tura likitoci daga asibitocin da ke Minna domin su taimaka wajen kula da wadanda suka jikkata da ke samun kulawa a  babban asibitin Suleja.

Daga Aliyu Lawal

Labarai

Labarai10 hours ago

Tinubu Ya Nada Ibrahim Masari a Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Harkokin Siyasa

Daga Bello Wakili Shugaban Ƙasa Bola Tinubu  ya naɗa Ibrahim Aminu Masari a matsayin Mai ba shi Shawara na Musamman...

Labarai11 hours ago

Kungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Wata ƙungiyar al’umma mai suna Hadejia Advocacy ta yaba wa Gwamnan  Jigawa, Umar Namadi, kan yadda...

Labarai17 hours ago

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Daga Yusuf Zubairu Kauru Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a...

Labarai18 hours ago

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar...

Labarai2 days ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi2 days ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai2 days ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai3 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai4 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Mafi Shahara