Labarai
Shugaba Tinubu Zai Tafi Ghana Bikin Rantsar Da Sabon Shugaban Kasa
Yau shugaba Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa Accra babban birnin jamhuriyar Ghana domin halartar bikin rantsar da zababben shugaban kasar John Dramani Mahama a ranar 7 ga watan Janairu.
Mahama, wanda ya zama shugaban kasar Ghana na 12 tsakanin shekarar 2011 zuwa 2017, an sake zabensa ne a watan Disambar 2024.
Zai gaji shugaba Nana Akufo-Addo, wanda ya yi mulki tsakanin 2017 zuwa 2025.
Sanarwar ta ce tafiyar Shugaba Tinubu zuwa Accra na zuwa ne bisa gayyatar zababben shugaban kasar, wanda ya kai masa ziyara a Abuja a farkon watan Disamba.
Sanarwar mai dauke da sa hannun mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Mista Bayo Onanuga, ta ce Mahama da shugaba Tinubu na da dadaddiyar alaka, kamar yadda Najeriya da Ghana ke da dadadden alaka tsakanin kasashen biyu.
Ta ce shugaba Tinubu, a matsayinsa na shugaban kungiyar ECOWAS, zai bi sahun sauran shugabannin kasashen Afrika wajen bikin.
Ya bayyana cewa Ministar Kasa a Ma’aikatar Harkokin Waje, Misis Bianca Odumegwu-Ojukwu da wasu manyan jami’an gwamnati za su raka shugaba Tinubu a wannan tafiya.
Bello Wakili/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
