Labaran Ketare
An kusa kulla yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza – Biden

Shugaba Biden ya ce akwai fatan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza nan da Litinin mai zuwa.
Kalaman shugaban Amurkan na zuwa ne yayin da rahotanni ke nuna alamun samun nasara a tattaunawar da ake yi tsakanin Isr’ila da Hamas ƙarƙashin jagorancin Qatar.
Da yake jawabi ga manema labarai a birnin New York, Mr Biden ya ce mai bashi shawara a kan tsaron ƙasa ya shaida masa cewa an kusa ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta, da kuma sakin mutanen da Hamas ta yi garkuwa da su.
Shugaba Biden ya ce bisa yadda abubuwa ke tafiya, nan da ranar Litinin za a sanar da batun tsagaita wutar.
Isra’ila da Hamas na ci gaba da tattauna yadda shirin tsagaita wutar zai kasance, a wani zama da wakilan ɓangarorin ke yi a Qatar.
Akwai rahotannin cewa za a sako fursunonin Falasɗinawa har 400 da ke tsare a Isra’ila, domin neman Hamas ta sako wa Isra’ilan mata 40, mafi yawan su dattijai ne.
Firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu dai ya sha alwashin ci gaba da shirinsa na luguden wuta a birnin Rafah da ke kudancin Gaza, ko da kuwa an cimma yarjejeniyar tsagaita wutar.
Can kuwa a gaɓar yamma da kogin Jordan, rahotanni sun ce an kashe Falasɗinawa uku a wata aran-gama da dakarun Isra’ila.
Hukumar lafiyar Falasɗinawan ta ce mutum aƙalla dubu huɗu aka kashe a gaɓar yamma da kogin Jordan tun da aka fara yaƙin a Gaza.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
