Connect with us

Fasaha

Sheikh Dahira Bauchi YA Sa Albarka Ga shirin Sa Ilimin Boko Ga Manhajar Makarantun Allo

Published

on

Fitaccen Malamin Addinin Musulunci a Bauchi Sheik Dahiru Usman Bauchi Ya Amince Da Hada Ilimin boko da Manhajin Almajiri.

 

Jagoran mabiya darikar Tijjaniya Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya ce yana goyon bayan shirin gwamnatin tarayya na sanya ilimin boko a cikin manhajar karatun makarantun Almajiri.

 

Ya bayyana haka ne a lokacin da Babban Sakataren Hukumar Almajiri da Ilimin Yara marasa Makaranta ta kasa NCAOOSCE Dr Muhammad Sani Idris ya ziyarce shi a Bauchi.

 

Sheikh Dahiru Bauchi ya ce kungiyar Tijjaniya ta dukufa wajen ganin ta aiwatar da duk wani tsari da zai inganta zamantakewa da tattalin arzikin kasar nan.

 

Tun da farko Sakataren zartarwa na NCAOOSCE ya shaida wa Shehin Malamin cewa ya je gidansa ne domin neman albarkar sa yayin da ya fara ziyarce ziyarce don sake fasalin karatun Almajirai tare da kwashe miliyoyin yaran da ba sa zuwa makaranta a kan tituna.

 

Ya kuma jaddada cewa hadakar za ta baiwa almajirai damar samun ilimi da fasaha don yin gogayya a duniya.

 

Dr Muhammad Sani Idris ya kuma ce shugaban kasa Bola Tinubu ya damu da matsalar almajirai da yaran da ba su zuwa makaranta kuma ba zai bar wata kafa da za ta bi don kawo karshen ta ba.

Alhassan Bauchi/Wababe

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara