Connect with us

Ilimi

Jihar Bauchi Za Ta Yi Aiki Da Hukumar Kula Da Almajirai Ta Kasa

Published

on

Gwamnatin jihar Bauchi za ta hada gwiwa da Hukumar Almajiri da Yara da basa zuwa Makaranta don daukar nauyin karatun yara marasa galihu.

 

Gwamna Bala Muhammad na jihar Bauchi ya bayyana kwarin gwiwar sabbin shugabannin Hukumar Almajirai da Ilimin Yara da ba su zuwa Makarantu na kasa wajen biyan bukatun yaran da abin ya shafa a kasar nan.

 

Ya bayyana hakan ne a lokacin da ya gana da Babban Sakataren Hukumar Dokta Muhammad Sani Idris wanda ya ziyarce shi a gidan gwamnati da ke Bauchi.

 

Gwamna Muhammad ya ce idan aka yi la’akari da tarihi da dimbin gogewar Sakataren Zartaswa, za a tunkari kalubalen Almajiri da yaran da ba sa zuwa makaranta.

 

A baya dai Sakataren zartaswar ya ziyarci Uwargidan Gwamnan Jihar Bauchi, Dakta Aisha Bala Muhammad wadda ta nemi goyon bayan hukumar wajen shigar da ilimin boko a cikin manhajar karatun almajirai karkashin aikinta na Pet project na gidauniyar AlMuhibba da kuma gidauniyar Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

 

Dokta Aisha Muhammad ta ce da irin dimbin gogewar da shugaban Hukumar Almajiri da Ilimin Yara da ba su zuwa Makarantu ke da ita, ta yi fatan hadin gwiwar da ake so da za ta tsara makomar miliyoyin yara masu rauni a kasar nan.

 

Sakataren zartarwa ya bayyana jin dadinsa da tarbar da aka yi masa a yayin ziyarar tare da bayar da tabbacin bada hadin kai don cimma manufofin.

 

Alhassan Usman/Wababe

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara