Connect with us

Fasaha

Sabuwar jami’ar Ilorin ta yaye dalibai karon farko su 146.

Published

on

 

Sabuwar jami’ar Muhammad Kamaludeen dake Ilorin ta yaye dalibai karon farko da suka su 146.

 

Da yake nasa jawabin shugaban jami’ar Farfesa Rasheed Jimoh ya bayyana cewa jami’ar ta bullo da wani kwas na zamani wanda zai baiwa sabbin dalibai sama da Dala dubu 1000 domin yiwa kamfanonin da suke son yi rijista domin bunkasa sana’o’insu.

 

Ya ce jami’ar ta bullo da wasu tsare-tsare da za su baiwa daliban damar yin tunani mai zurfi don ba su damar gogayya da sauran kamfanonin kasashen duniya.

 

Shugaban jami’ar ya bayyana cewa daya daga cikin irin wadannan tsare-tsare shi ne samar da sabbin kwasa-kwasai da samar da ra’ayoyi don baiwa dalibai tun daga zangon karatunsu na farko da sana’o’in da suka dace da kuma sabbin dabaru .

 

Farfesa Jimoh ya lura cewa jami’ar za ta sauƙaƙe rajistar kamfanonin ta hanyar Hukumar yiwa kamfanoni rijista (CAC) da kuma taimaka wa don haɓaka ta hanyar saka hannun jari a kamfanonin.

 

Ya ce jami’ar dai tana da kwasa-kwasai 15 da hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta amince da su.

 

A nasa jawabin, Uban jami’ar kuma Mai Martaba Sarkin Ilọrin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari ya bukaci masu neman shiga jami’a da su yi amfani da irin kwasa-kwasan da sabuwar jami’ar ta ke da su.

 

Mai martaba Sarkin ya mika godiyarsa ga wanda ya assasa kungiyar Ansarul Islam Society of Nigeria, Marigayi Sheikh Muhammad Kamaldeen Al- Adabbiy bisa hada ilimin addinin musulunci da ilimin zamani wanda a karshe ya kai ga kafa jami’a a tunawa da shi.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU/Wababe

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara