Labarai
Za A Gudanar Da Taron Masana Harkokin Yada Labarai Karo Na 2 A Kano
Daga Khadijah Aliyu
An fara shirye-shirye gudanar da taron shekara-shekara karo na 2 da bikin shigar da sabbin mambobi na Ƙungiyar Masana Harkokin Yada Labarai ta Najeriya (SNB), bayan an kaddamar da Kwamitin Shirya Taron (LOC) a Kano.
An tsara gudanar da taron ne daga ranar 20 zuwa 21 ga watan Nuwamban 2025.
Shugaban Ƙungiyar, Farfesa Umaru A. Pate, ya umarci kwamitin da ya gudanar da aikinsa da himma da jajircewa domin tabbatar da nasarar taron, wanda shi ne irinsa na farko da za a yi a Kano.
Ya bayyana cewa ana sa ran masana sama da 400 da sabbin mambobi daga ciki da wajen jihar za su halarta.
Farfesa Pate ya yaba wa Gwamnatin Jihar Kano kan jajircewarta wurin inganta aiki da ɗabi’a a harkar yada labarai, yana mai cewa taron zai kasance muhimmiyar dama wacce za ta ƙara ɗaukaka martabar jihar a fagen kafofin yaɗa labarai.
A nasa jawabin, Shugaban LOC, Alhaji Ado Salisu Warawa, ya nuna godiya ga jagorancin ƙungiyar na ƙasa bisa amincewa da kwamitin, yana mai tabbatar da cewa za su gudanar da taron cikin cikakkiyar nasara.
Rel/Khadijah Aliyu
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
