Connect with us

Labarai

Wani Fasinja Ya Yi Kashin Sama Da Dauri 100 Na Hodar Ibilis- NDLEA

Published

on

Hukumar yaki da safarar miyagun kwayoyi a Najeriya NDLEA ta ce yanzu haka ta na rike da wani fasinjan jirgin saman dake kan hanyar zuwa birnin Paris ta kasar Faransa saboda zargin mallakar hodar ibilis,  inda ya yi  kashin dauri dari daya da goma sha daya na hodar da ya hadiye a cikinsa bayan an kama shi.

Mai magana da yawun hukumar Femi Babafemi yace sun kama wannan mutumin mai suna Emmanuel Okechukwu Orjinze ne a tashar jiragen saman Abuja lokacin da yake kokarin tsallake wuraren binciken fasinjoji domin hawa jirgin sama.

Okechukwu ya shaidawa NDLEA cewar shi ‘dan kwallo ne a Turai lokacin da aka kama shi a ranar 21 ga wannan wata a daidai lokacin da yake kokarin hawa jirgin Air France mai lamba 878 dake shirin barin Abuja zuwa Paris.

Wanda ake zargi, Emmanuel Okechukwu Orjinze
Emmanuel Okechukwu Orjinze

Bayan gudanar da bincike a kansa da na’ura, an tabbatar da cewar akwai tarin kunshin hodar ibilis wato cocaine a cikin sa, abin da ya sa aka tsare shi na tsawon kwanaki 3 kuma aka yi sa’ar ganin ya yi kashin wadannan dauri 111 da nauyin su ya kai kilo  1,603.

Yanzu dai haka Okechukwu na can a tsare inda ake sa ran gabatar da shi a gaban kotu domin amsa tambayoyin hukumomin shari’a.

Babafemi ya kuma bayyana nasarar da hukumar NDLEA ta samu na tarwatsa wata kungiya ta masu hadahadar  miyagun kwayoyi a tashar jiragen saman Lagos, tare da kama mutane 4  daga cikin su da kuma kwace kilo 8 na hodar methamphetamine da kilo 7 da rabi na kwayar da ake kira cloud da ake safarar ta daga kasar Afirka ta kudu.

Jami’in yace ya yin gudanar da bincike, an kuma kama wasu karin mutane 2 a unguwar rukunin gidajen dake Ajao Estate dake birnin na Lagos.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara