Connect with us

Labarai

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Published

on

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido daga Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON domin tantance ayyukan hukumar.

A jawabin shugabar tawagar kuma  babbar jami’ar  hukumar ta NAHCON a jihar Jigawa Hajiya Rabi’atu Dahiru Nyako, ta bayyana cewa manufar ziyarar ita ce tantance kayayyakin aikin hukumar tare da duba yaddatake gudanarda shirye-shiryen aikin Hajjin bana.

Tawagar za ta tantance kayan aiki, da shirye-shiryen jigilar maniyyatan jihar, da takardun tafiya kasa mai tsarki, da fasfo fasfo da sauransu”.

Babbar Jami’iar ta bayyana gamsuwa da irin shirye-shiryen da hukumar ta yi.

 

A nasa jawabin, babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana cewa, an samu nasarori da dama a kan shirye-shiryen gudanar da aikin hajjin shekarar 2024 a jihar.

Shugaban hukumar ya kara da cewa, hukumar ta kara wa’adin  gudanar da lakcocin aikin hajji ga maniyyatan da ke fadin kananan hukumomi ashirin da bakwai na jihar.

Ya nanata kudurin gwamnatin jihar na tabbatar da jin dadin Alhazan  Jigawa tun daga gida Najeriya har zuwa kasar Saudiyya.

Labbo ya yabawa NAHCON bisa ci gaba da bayar da goyon baya da hadin kai ga hukumar domin samun nasarar aikin Hajjin na bana.

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, tawagar ta duba sashin amfani da na’ura mai kwakwalwa, da ayyukan da ake gudanarwa, tare da wasu  gine-gine da aka gyara, da  sauran kayayyakin zamani na hukumar.

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara