Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai Ta Kasa Ta Sanar Da Kudin Aikin Hajjin Bana

Published

on

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da kudin aikin Hajjin shekarar 2025.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun
Mataimakiyar Daraktan Watsa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara.

Ta ce “Hukumar aikin Hajji ta kasa (NAHCON), a karkashin jagorancin shugabanta, Farfesa Abdullahi Saleh Usman na farin cikin sanar da kudin aikin Hajjin shekarar 2025”.

Ta ce an sanar da kudin kujerar na bana ne bayan amincewar ofishin mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima.

Ta kara da cewa “Hakika Shugaban Hukumar NAHCON da tawagarsa tare da hadin guiwar wakilin fadar shugaban kasa, Malam Ameen Amshi, wanda shi ne mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan ayyuka na musamman, sun yi  kokari matuka wajen ganin an biya kudin aikin Hajji daidai da yadda aka biya a bara.

“Maniyyata aikin Hajjin 2025 daga shiyyar Borno da Adamawa, za su Naira miliyan 8,327,125.59 (miliyan takwas, da dubu dari uku da ashirin da bakwai, da dari daya da ashirin da biyar da kwabo hamsin da tara).

“Hakazalika, maniyyata daga jihohin Kudu za su biya Naira miliyan 8, 784, 085.59 (miliyan takwas, da dubu dari bakwai da tamanin da hudu, da Naira tamanin da biyar Naira kobo hamsin da tara).

“Alhazan da suka fito daga shiyyar Arewa kuma za su biya Naira 8, 457,685.59 (miliyan takwas, da dubu dari hudu da hamsin da bakwai, da dari shida da tamanin da biyar da kwabo hamsin da tara).”

Fatima Usara ya ce Farfesa Saleh ya yaba wa daukacin tawagar, inda ya bayyana kudin aikin Hajjin a matsayin wani babban hadin gwiwa da duk masu ruwa da tsaki.

Ya yaba da goyon bayan fadar shugaban kasa da kungiyar sakatarorin gudanarwa na jihohi.

Shugaban ya bukaci maniyyatan da suke son zuwa aikin Hajji da su lura da ka’idoji hukumar da na kasar Saudiyya, tare da jaddada mahimmancin biyan kudi da wuri da kuma yin rajista a kan lokaci don guje wa matsaloli.#Hajj2024

 

Safiyah Abdulkadir

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara