Labarai
Muna Yankin Arewacin Kaduna Ba Kudancin ta ba – Al’ummar Lere
Wadansu Masu kishin Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna sun karyata rade radin dake yawo cewa Lere tana sashin Kuduncin Kaduna ne.
Bayanin haka na kunshe ne a cikin sanarwar da Shugaban gamayyar kungiyoyin Karamar Hukumar Barrista Nasiru Bello Dembo da Sakataren sa Mal. Ahmed Idris suka sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai a Kaduna.
Sanarwar ta bayyana cewa an buga rade radin ne a jaddawalin littafin taron shekara shekara da Kungiyar al’ummar Kudancin Kaduna SOKAPU ta shirya na bana.
Sanarwar tace anga sunaye da hotunan wasu masu rike da mukaman siyasa daga Karamar Hukumar Leren da cewa wakilai ne daga Kudancin Kaduna, lamarin data karyace tsagwaro kuma bashi da tushi balle makama.
A cewar sanarwar wannan ya sabawa sashi na 8 da 48 da kuma 72 na tsarin mulkin Nigeria Wanda ya sanya Lere a mazabar ‘Dan majalisar Dattawa na Arewacin Jihar Kaduna.
Sanarwar ta Kara da cewa Karamar Hukumar Lere bata da wata alaka da sashin Kudancin Kaduna kana ta gargadi wadanda suka shirya taron kada su sake yin haka anan gaba domin gudun Kawo rudami a cikin al’umma.
REL/LERE
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
