Ilimi
Jihar Kebbi Za Ta Biya Kudin Makaranta Naira Miliyan 585 Ga Dalibanta Da Ke Indiya
Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasir Idris, ya amince da fitar da Naira miliyan 585 domin biyan kudin karatu na ‘yan asalin jihar 100 da ke karatu a jami’o’i daban-daban na kasar Indiya.
Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar Isa Abubakar Tunga, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai, ya bayyana cewa hakan na daga cikin kokarin gwamnan jihar na bunkasa ilimi da kyawawan dabi’u a makarantun gaba da sakandare.
Ya bayyana cewa, nan ba da dadewa ba gwamnatin jihar za ta bai wa daliban da ke karatu a Masar kudaden tallafin karatu saboda suna karkashin kulawar tallafin karatu na na kasar Misra.
Abdullahi Tukur
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
