Labarai
Mazauna Sabon Gero Sun Koka Kan Watsi Da Aikin Gyaran Hanyarsu
Mazauna unguwar Sabon Gero, dake bayan Millennium City a Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, sun roƙi gwamnatin jihar da ta gaggauta kammala aikin gyaran titin unguwar, wanda suka ce an bar shi a cikin mawuyacin hali duk da cewa an bai wa wani kamfani aikin kusan shekara guda da ta gabata.
Mazauna yankin sun bayyana cewa halin da hanyar take ciki ya jefa su cikin matsanancin rayuwa, musamman mata masu juna biyu da ke tilasta musu hawa babura domin neman kulawa a wajen unguwar, kasancewar babu asibiti a yankin.
Ɗaya daga cikin mazauna, Rashida Shehu, wadda ke da juna biyu, ta ce ta ji rauni a lokacin da take kokarin bin hanyar zuwa gari domin kula da lafiya, inda ta roƙi gwamnati ta taimaka musu cikin gaggawa.
Haka kuma, rashin makarantar gwamnati a Sabon Gero ya sanya yaran mazauna yankin cikin wahala, saboda da dama daga cikinsu ba sa iya jure tafiyar neman ilimi zuwa waje.
Manoma kuma sun koka kan yadda rashin titin ke hana su kai kayayyakin gona kasuwa.
Mai unguwar Sabon Gero, Mai Anguwa Sunusi, ya bayyana cewa tun shekara guda da ta gabata aka bai wa kamfanin gyaran hanya na Think Lab aikin, amma har yanzu babu wani ci gaba da aka gani a wajen.
Ya roƙi gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, da ya sanya wa aikin titin muhimmanci don amfanin al’umma da jihar baki ɗaya.

A nasa bangaren, matasa ƙarƙashin kungiyar cigaban Sabon Gero sun yi barazanar gudanar da zanga-zangar lumana idan aka ci gaba da yin shiru kan aikin, inda suka ce jinkirin kammalawa ya jawo tsaikon ci gaba tare da jefa al’umma cikin haɗari da matsalolin tsaro.
’Yan kasuwa da masu sana’o’i a yankin sun kuma ce lalacewar titin ta rage masu ciniki, tare da hana masu saka jari daga wajen zuwa yin kasuwanci a Sabon Gero.
A cewar su, wannan yanayi ya sabawa alkawuran gwamnati na samar da ci gaban kowa da kowa, abin da ya sa suke jin an nuna musu wariya.
COV: Khadija Kubau
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
