Labarai
Matashiya Ta Harbe Kanta A Ofishin ‘Yan Sandan Amurka
Wata budurwa ta harbe kanta har lahira da bindiga mallakar maitaimakin babban sufeton ‘yan sanda a harabar wani ofishin ‘yan sanda da ke California.
Matashiyar, wacce ba a bayyana sunanta ba, ta isa wurin ne inda ta fara buga kofar ofishin na ‘yan sanda da ke kusa da birnin Los Angeles.
Yayin da jami’an suka je bude kofa, matashiyar ta yi nasarar kwace wata bindiga daga daya daga cikinsu.
A cikin wata sanarwa fa ya fitar, Ofishin ‘yan sanda na gundumar Los Angeles ya ce “matashiyar ta kutsa cikin harabar ofishin ne inda ta kai hannun ta kwato bindigar mataimakin sufeton.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, an yi gwagwarmaya tsakanin mataimakan sufeton da matashiyar da ta yi nasarar zare masa bindiga, inda ya yi kokarin kwacewa.
A lokacin gwagwarmaya, matashiyar ta raunata kanta da bindiga,inda ta mutu nan take a cewar ma’aikatan lafiya da suka isa wurin.
Jami’an ke bincike sun ce sun fara binciken ne biyo bayan kiran iyayen matashiyar wadanda suka rene ta, inda suka kira don ba da rahoton cewa tana fama da matsalar tabin hankali.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
