Labarai
Hukumar Alhazai Ta Birnin Tarayya Ta Bai Wa Alhazai Zabi
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Babban Birnin Tarayya Abuja ta bukaci maniyyatan da ke son a mayar musu da kudaden aikin Hajji da suka biya sakamakon karin da aka yi, da su gabatar mata da bukatar hakan.
Jami’in Hulda da Jama’a na Hukumar Muhammad Lawal Aliyu ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai.
Muhammad Aliyu ya ce Maniyyatan da suka riga suka biya Nera Miliyan Hudu da Dubu Dari Shida da Casa’in da Tara, za su cikasa Nera Miliyan Daya da Dubu Dari Tara da Goma sha Takwas nan da ranar 27 ga watan Maris 2024, domin samun damar gudanar da aikin Hajjin.
Hakan a cewarsa ya yi daidai da sabon umurnin da Hukumar Alhazai ta Kasa ta bayar.
“Don haka dukkan maniyyatan da suka riga suka biya kudi a baya, za su kara biyan kumanin Nera Milyan Biyu, yayin da wadanda ba su biya ko sisi ba, za su biya jimillar Nera Miliyan Takwas da Dubu Dari Biyu da Hamsin da Hudu kafin cikar wa’adin. “Inji shi.
Hukumar ta shawarci wadanda ke son a mayar musu da kudadensu da su rubuta bukatar hakan ga Daraktan hukumar ta babban birnin tarayya Abuja tare da bayanan asusun ajiyarsu na banki domin a dawo musu da kudaden, ko kuma su dage tafiyarsu zuwa shekara mai zuwa.
-
Labarai7 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai20 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai20 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati