Labarai
Matashiya Ta Harbe Kanta A Ofishin ‘Yan Sandan Amurka
Wata budurwa ta harbe kanta har lahira da bindiga mallakar maitaimakin babban sufeton ‘yan sanda a harabar wani ofishin ‘yan sanda da ke California.
Matashiyar, wacce ba a bayyana sunanta ba, ta isa wurin ne inda ta fara buga kofar ofishin na ‘yan sanda da ke kusa da birnin Los Angeles.
Yayin da jami’an suka je bude kofa, matashiyar ta yi nasarar kwace wata bindiga daga daya daga cikinsu.
A cikin wata sanarwa fa ya fitar, Ofishin ‘yan sanda na gundumar Los Angeles ya ce “matashiyar ta kutsa cikin harabar ofishin ne inda ta kai hannun ta kwato bindigar mataimakin sufeton.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, an yi gwagwarmaya tsakanin mataimakan sufeton da matashiyar da ta yi nasarar zare masa bindiga, inda ya yi kokarin kwacewa.
A lokacin gwagwarmaya, matashiyar ta raunata kanta da bindiga,inda ta mutu nan take a cewar ma’aikatan lafiya da suka isa wurin.
Jami’an ke bincike sun ce sun fara binciken ne biyo bayan kiran iyayen matashiyar wadanda suka rene ta, inda suka kira don ba da rahoton cewa tana fama da matsalar tabin hankali.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United