Labarai
Najeriya Ta Cimma Sabon Tsarin Hadin Gwiwa Kan Sha’anin Tsaro da Amurka
Daga Bello Wakili
Gwamnatin Tarayya ta ce tattaunawa da tawagarta ta yi da jami’an Amurka ta kara karfafa huldar tsaro tsakanin kasashen biyu tare da bude sabbin hanyoyin hadin gwiwa domin kara kare ‘yan Najeriya.
Tawagar, karkashin jagorancin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, ta gana da manyan jami’an Majalisar Dokokin Amurka, Ofishin Bangaren Addini na Fadar White House, Ma’aikatar Harkokin Waje, Majalisar Tsaro ta Kasa da Ma’aikatar Yaki a birnin Washington DC
A yayin tattaunawar, tawagar ta musanta zargin kisan kare dangi a Najeriya, tana mai jaddada cewa hare-haren da ake samu na shafar al’umma ne daga bangarori daban-daban na kabilu da addinai. Ta ce irin wannan kuskuren fassarar halin da ake ciki na haifar da rarrabuwar kai da kuma karkatar da gaskiyar abin da ke faruwa.
Bayan ganawar, Gwamnatin Amurka ta tabbatar da kudirinta na karfafa huldar tsaro da Najeriya ta hanyar inganta musayar bayanan sirri, hanzarta aiwatar da bukatun kayan aikin tsaro, tare da yiwuwar bayar da karin kayan tsaro na musamman idan sun samu, domin tallafa wa yakin da ake yi da ‘yan ta’adda da kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi.
Amurka ta kuma nuna shirinta na bada tallafin jin kai ga al’ummomin da rikici ya shafa a yankin Arewa ta tsakiya, da kuma taimakawa wajen karfafa tsarin ankararwa da wuri, tare da daukar mataki cikin gaggawa.
Kasashen biyu sun amince da fara aiki kai tsaye da wata yarjejeniyar hadin gwiwa da kafa Kwamitin Aiki na Hada-hadar Tsaro domin tabbatar da tsari guda wajen aiwatar da abin da aka cimma.
A nata bangaren, Najeriya ta sake nanata kudirinta na inganta tsarin kare fararen hula a fadin kasar.
Gwamnatin Tarayya ta ce tattaunawar ta bayar da dama wajen gyara kuskuren fahimta game da halin da ake ciki, ta karfafa amincewar juna, tare da inganta dabarun hadin gwiwa domin kare al’ummomi masu rauni musamman a yankin Arewa ta Tsakiya.
Mambobin tawagar sun hada da Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi; Shugaban Hafsoshin Tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Daraktan Leken Asiri na Soji, Laftanar Janar Emmanuel Parker Undiandeye; Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Egbetokun; Daraktan Harkokin Ketare a Ofishin mai bai wa Shugaban Kasa shawara kan harkokin tsaro NSA, Ambasada Ibrahim Babani; da Mai Baiwa NSA Shawara ta Musamman, Ms. Idayat Hassan.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
