Labarai
Manyan Alkalai Sun Bukaci Birtaniya Ta Daina Siyar wa Isra’ila Makamai

Tsofaffin alƙalan kotun ƙoli sun bi sahun masana shari’a fiye da 600 wajen kira ga gwamnatin Birtaniya ta daina sayar wa Isra’ila makamai.
Cikin wata takarda zuwa ga firaiminista Rishi Sunak, tsofaffin alƙalan sun ce dole ne a kawo ƙarshen fitar da makamai saboda Birtaniya na cikin haɗarin karya dokokin duniya.
Tuni dai mista Sunak yake fuskantar matsin lamba bayan sojojin Isra’ila sun kashe wasu ma’aikatan agaji bakwai.
A ranar Talata ne, firaiministan ya ce Birtaniya tana da wani tsari na kaffa-kaffa game da lasisin makamai.
Tsohuwar shugabar kotun ƙoli, Lady Hale na cikin masana sama da 600 da suka sa hannu kan takardar mai shafuka 17.
Takardar ta ce akwai buƙatar a ɗauki mataki na gaske domin hana Birtaniya faɗawa matsalar karya dokokin ƙasa da ƙasa har da yiwuwar saɓa yarjejeniyar da ta shafi dokokin kisan kiyashi.
Sauran mutanen da suka sa hannu kan takardar sun haɗa da tsofaffin alƙalan kotun ƙoli Lord Sumption da Lord Wilson tare da wasu alƙalai tara da manyan lauyoyi 69.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
