Connect with us

Ilimi

Malaman Jami’ar Kwara Sun Yi Zanga-Zangar Lumana

Published

on

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Kwara da ke Malete (KWASU), ta gudanar da zanga-zangar lumana a ranar Laraba domin neman a biya su kudaden alawus-alawus na EAA da  sauran hakkokinsu.

Malaman a karkashin inuwar ASUU sun ce sun shiga sahun sauran rassan kungiyar a fadin ƙasa wajen matsa lamba kan gwamnatin tarayya da ta aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma tsakaninta da ASUU tun shekarar 2009.

Shugaban  ASUU reshen KWASU, ya bayyana cewa jinkirin biyan EAA da sauran hakkoki ya sanya malamai cikin mawuyacin hali, inda da yawa daga cikinsu ke fama da matsalolin tattalin arziki.

Ya ce duk da ƙalubalen da suke fuskanta, malamai na ci gaba da gudanar da ayyukansu na koyarwa da bincike, sai dai yanzu tura ta kai bango.

Mun fito ne domin nuna damuwarmu da kuma jawo hankalin gwamnati. Babu shakka, ci gaban ilimi ba zai yiwu ba idan malamai ba su samu kulawa da gata ba,” In ji shi.

Kungiyar ta kuma yi kira ga Gwamnan Jihar Kwara da ya yi wajen ganin an warware matsalar cikin gaggawa.

ASUU ta yi gargadin cewa, idan aka ci gaba da watsi da bukatunsu, ba za su yi jinkiri ba wajen ɗaukar matakan da suka fi wannan tsauri a nan gaba.

Ta yi kira ga ɗalibai, iyaye da sauran jama’a da su fahimci matsayin da suke ciki, tare da goya musu baya wajen kare martabar ilimi da neman hakkinsu.

 

Ali Muhammad Rabi’u

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara