Ilimi
Malaman Jami’ar Kwara Sun Yi Zanga-Zangar Lumana
Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Kwara da ke Malete (KWASU), ta gudanar da zanga-zangar lumana a ranar Laraba domin neman a biya su kudaden alawus-alawus na EAA da sauran hakkokinsu.
Malaman a karkashin inuwar ASUU sun ce sun shiga sahun sauran rassan kungiyar a fadin ƙasa wajen matsa lamba kan gwamnatin tarayya da ta aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma tsakaninta da ASUU tun shekarar 2009.
Shugaban ASUU reshen KWASU, ya bayyana cewa jinkirin biyan EAA da sauran hakkoki ya sanya malamai cikin mawuyacin hali, inda da yawa daga cikinsu ke fama da matsalolin tattalin arziki.
Ya ce duk da ƙalubalen da suke fuskanta, malamai na ci gaba da gudanar da ayyukansu na koyarwa da bincike, sai dai yanzu tura ta kai bango.
“Mun fito ne domin nuna damuwarmu da kuma jawo hankalin gwamnati. Babu shakka, ci gaban ilimi ba zai yiwu ba idan malamai ba su samu kulawa da gata ba,” In ji shi.
Kungiyar ta kuma yi kira ga Gwamnan Jihar Kwara da ya yi wajen ganin an warware matsalar cikin gaggawa.
ASUU ta yi gargadin cewa, idan aka ci gaba da watsi da bukatunsu, ba za su yi jinkiri ba wajen ɗaukar matakan da suka fi wannan tsauri a nan gaba.
Ta yi kira ga ɗalibai, iyaye da sauran jama’a da su fahimci matsayin da suke ciki, tare da goya musu baya wajen kare martabar ilimi da neman hakkinsu.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
