Connect with us

Labarai

Mai Martaba Sarkin Kauru Ya Kara Ankarar Da Al’ummarsa Kan Matsalar Tsaro

Published

on

Mai martaba Sarkin Kauru a Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u na biyu, ya kara  fadakar da al’ummar masarautarsa game da matsalar tsaro, duba da yadda ake  samun yawaitar satar mutane da ayyukan ‘yan bindiga a jihar.

 

Mai Martaba Alhaji Zakari Ya’u II, wanda ya bayyana haka a wajen taron buda baki na watan Ramadan na shekara-shekara a fadarsa da ke Kauru, ya jaddada muhimmancin yin taka tsantsan da hadin gwiwa da jami’an tsaro domin yakar kalubalen tsaro da ake fuskanta.

 

Mai Martaba Sarkin Kauru Alhaji Zakari Ya’u II

 

Sarkin ya kuma jaddada hakkin da ya rataya a wuyan ‘yan kasa wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a tsakanin al’umma, tare da yin kira da a hada kai domin tunkarar wadannan matsalolin yadda ya kamata.

Ya kuma nanata kiransa na ci gaba da hada kai da jami’an tsaro,  yana mai karfafa gwiwar mazauna yankin da su bayar da gudunmawarsu wajen inganta wayar da kan al’umma ta fuskar tsaro da kuma samar da yanayi mai kyau ga kowa da kowa.

Alhaji Zakari Ya’u II, ya kuma jinjinawa daukacin wadanda suka halarci taron buda bakin na shekara shekara, yana mai nuna jin dadinsa bisa hakan, domin wata hanya ce ta sada zumunci a cikin watan Ramadan.

Da yake tsokaci game da mahimmancin taimako kuwa, Sarkin ya gabatar da wani hadisi da ke jaddada taimakon juna a tsakanin al’umma, inda ya bukaci jama’a da su kara jaiki wajen kara karfafa hakkin makwafta da kuma samar da zaman lafiya a cikin al’umma.

Hakazalika Martaba Alhaji Zakari Ya’u II, ya  yi addu’ar samun albarkar watan Ramadan ga dukkan mahalarta taron da iyalansu.

(Na tsakiya) Sakataren Majalisar Masarautar Kauru, Malam Muhammad Sani Suleiman (Dan buran Kauru)

 

A yayin taron, Sakataren Majalisar Masarautar, Malam Muhammad Sani Suleiman wanda shi ke rike da sarautar Dan Buran na Kauru, ya bayyana irin sadaukarwar da Sarkin yakeyi wajen tabbatar da jin dadin al’ummarsa da kuma tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a masarautarsa.

 

Yusuf Zubairu

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara