Kasuwanci
Kwara Ta Ware Naira Miliyan Dubu Biyar Don Kula Da Cibiyoyin Lafiyar Jihar
Gwamnatin jihar Kwara ta ware naira biliyan 5 domin inganta cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 70 a kananan hukumomin uku na jihar.
Babban Sakatariyar Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Kwara (KWHCDA), Farfesa Nusirat Elelu ce ta bayyana haka a lokacin rattaba hannu kan kwangilolin da aka yi a hedikwatar Hukumar da ke Ilorin.
Ta ce matakin zai hada da inganta ababen more rayuwa, samar da lantarki ta amafani da hasken rana, da samar da wuraren zama na ma’aikata, da samar da ruwan sha da samar da kayan aikin asibiti na zamani a duk wuraren da ke amfana da cibiyoyin kiwon lafiya na farko.
Farfesa Elelu ya bayyana cewa shiga tsakani na zuwa ne tare da tallafin da Bankin Duniya ke tallafawa.
Ta yi nuni da cewa shirin zai sa cibiyoyin kula da lafiya matakin farko su kasance masu inganci don samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya a matakin farko a fadin jihar.
Kwamishinan ya ce gaba daya makasudin shi ne a mayar da dukkan cibiyoyin PHC ‘daidai da manufa’ tunda tsarin PHC shi ne farkon tuntuɓar tsarin kiwon lafiyar ƙasa.
Farfesa Elelu ya roki duk wadanda suka yi nasara da su tabbatar sun samar da ingantattun ayyuka don tabbatar da amanar da aka ba su.
A nasa bangaren manajan shirin na IMPACT, Dr. Michael Oguntoye, ya ce za a bayar da kwangilar ne cikin watanni 3 kuma jihar ba za ta lamunci tsaikon wajen aiwatar da aikin ba.
Dr.Oguntoye ya kara da cewa wadanda suka fara cin gajiyar shirin na IMPACT su ne yara da mata ‘yan kasa da shekaru biyar, inda ya ce aikin zai kuma inganta samar da ayyukan kiwon lafiya ga daukacin mazauna jihar.
Cov/Ali Muhammad Rabiu/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
