Connect with us

Labarai

Kebbi: An Samu Asarar Rayuka a Rikicin Alwasa

Published

on

Daga Sani Dutsinma

Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Kebbi ta ce an dawo da zaman lafiya a ƙauyen Alwasa da ke Ƙaramar Hukumar Argungu.

Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

Ya ce ƙauyen Alwasa na cikin kulawar tsaro, biyo bayan gaggauta tura jami’an ‘yan sanda tare da ƙarin dakaru, waɗanda ke kan aiki domin sa ido kan yanayin tsaro, tabbatar da doka da oda, da kuma hana sake ɓarkewar rikici.

A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a lokacin bikin Sallah, inda rikici ya ɓarke tsakanin wasu matasa, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka, yayin da wasu suka  jikkata, wadanda a halin yanzu suke samun kulawa a Asibitin Gwamnati na Argungu.

Bayan wannan, an samu harin ramuwar gayya wanda ya haifar da ƙarin asarar rayuka. Rundunar ‘yan sandan ta ce ta fara gudanar da cikakken bincike kan lamarin, tare da ƙoƙarin gano da kama duk waɗanda ke da hannu a ciki.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, CP Umar Mohammed Hadejia, ya yi Allah-wadai da lamarin, tare da gargadin cewa duk wanda aka samu da hannu cikin aikata laifi ko tayar da tarzoma zai fuskanci fushin hukunma.

Ya kuma buƙaci mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu, su guji yaɗa jita-jita, su kuma kauce wa ɗaukar doka a hannunsu, yana mai cewa za a ci gaba da sanar da jama’a.

Labarai

Ilimi13 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara