Connect with us

Kasuwanci

Karamar Hukumar Sule Tankarkar Ta Raba Kayayyakin Tallafi Ga Al’ummarta

Published

on

Gwamnatin Jihar Jigawa ta yaba da shirin tallafawa al’umma da Shugaban karamar hukumar Sule Tankarkar ya bullo da shi a yankin.

Gwamnan Jihar, Mallam Umar Namadi ya bayyana haka a lokacin da ya halarci taron kaddamar da rabon tallafin da aka gudanar a karamar hukumar.

Malam Umar Namadi, ya bayyana matukar jin dadinsa bisa wannan gagarumin tallafi, da ya haɗa da bayar da kayayyaki da jari ga rukunin al’umma daban-daban.

Yana mai nuni da cewar, wannan mashahurin shiri ya nuna kyakkyawan hangen nesa na Shugaban karamar hukumar, Alhaji Tasi’u Adamu, wajen tallafa wa mutanen karkara da ke fama da kalubale daban daban.

Namadi, ya kaddamar da rabon tallafi ga mutane fiye da 350 a karamar hukumar Sule Tankarkar.

Wakilinmu ya aiko mana da rahoton cewar, an gudanar da rabon tallafin wanda ya hada da tallafin karatu ga matasa 80 da aka sama musu guraben karatu a manyan jami’o’i da kwalejoji a faɗin kasar nan, da rabon babura ga mutane 30, sai keken ɗinki da aka rabawa mata 30.

Kazalika, an raba kekunan hawa 30 ga ɗalibai, da injin niƙa guda 10 da aka rabawa matsakaitan ‘yan kasuwa.

Sai kuma tallafin jari na naira dubu dari 2 da aka rabawa ‘yan kasuwa har su  20 da tallafin jari na naira dubu 100 ga ƙananan ‘yan kasuwa guda 20.

Sauran su ne tallafin jari na naira dubu hamsin hamsin ga mutane 30, da kuma bayar da naira dubu ashirin ashirin ga mutane 100, domin rage radadin halin da ake ciki, da rabon shagunanan tafi da gidanka guda 3 ga matasa masu kasuwanci.

Har ila yau, an raba babura masu kafa 3, na daukan kaya guda 2 ga matasa, sai kuma bayar da mukullin gidaje masu ɗaki biyu ga matasa guda 4 daga sassa daban-daban na karamar hukumar Sule Tankarkar.

A don haka, Gwamnan ya yi kira ga sauran shugabannin ƙananan hukumomi na jihar da su yi koyi da irin wannan gagarumin aikin  na Tasiu Adamu domin al’umma su ci gaba da sharbar romon mulkin dimokradiyya.

Ya bayyana cewar irin waɗannan ayyuka ne ke taka muhimmiyar rawa wajen rage talauci da samar da ayyukan yi ga jama’a.

Taron ya samu halartar jama’a daga sassa daban-daban na jihar, inda aka bayyana wannan shiri a matsayin abin alfahari ga al’ummar Sule Tankarkar da Jihar Jigawa baki daya.

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara