Connect with us

Labarai

Jigawa: Hukumar Alhazai ta Yaba da Naɗin Sarkin Dutse Amirul Hajjin 2026

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa naɗa Mai Martaba Sarkin Dutse, Alhaji Hamim Muhammadu Sanusi a matsayin jagoran Alhazan jihar a aikin Hajjin shekarar 2026.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Alhaji Habibu Yusuf Adamu, ya fitar ga manema labarai a Dutse.

Ya bayyana cewa, Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya ce naɗin ya dace ƙwarai, la’akari da jajircewar Sarkin wajen harkokin addini da kuma rawar da yake takawa a matsayin babban jagoran al’umma a Jihar Jigawa.

Ahmed Labbo ya jaddada cewa Amirul Hajj na shekarar 2026 yana da cikakken ilimin addini da ya dace domin jagorantar tawagar jihar.

Ya kuma yi alƙawarin yin aiki kafaɗa da kafaɗa da Amirul Hajjin, tare da neman shawararsa a matsayin jagoran al’umma kan duk wasu lamurra da za su taso yayin gudanar da aikin.

Darakta Janar ɗin, a madadin ma’aikatan hukumar, ya miƙa saƙon taya murna ga Amirul Hajji, tare da tabbatar da aniyar ma’aikatansa na yin aiki tare.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya naɗa Sarkin Dutse a matsayin Amirul Hajj domin jagorantar Alhazan jihar zuwa ƙasar Saudiyya a aikin Hajjin shekarar 2026.

 

 

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara