Labarai
Jigawa: Hukumar Alhazai ta Yaba da Naɗin Sarkin Dutse Amirul Hajjin 2026
Daga Usman Muhammad Zaria
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa naɗa Mai Martaba Sarkin Dutse, Alhaji Hamim Muhammadu Sanusi a matsayin jagoran Alhazan jihar a aikin Hajjin shekarar 2026.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Alhaji Habibu Yusuf Adamu, ya fitar ga manema labarai a Dutse.
Ya bayyana cewa, Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya ce naɗin ya dace ƙwarai, la’akari da jajircewar Sarkin wajen harkokin addini da kuma rawar da yake takawa a matsayin babban jagoran al’umma a Jihar Jigawa.
Ahmed Labbo ya jaddada cewa Amirul Hajj na shekarar 2026 yana da cikakken ilimin addini da ya dace domin jagorantar tawagar jihar.
Ya kuma yi alƙawarin yin aiki kafaɗa da kafaɗa da Amirul Hajjin, tare da neman shawararsa a matsayin jagoran al’umma kan duk wasu lamurra da za su taso yayin gudanar da aikin.
Darakta Janar ɗin, a madadin ma’aikatan hukumar, ya miƙa saƙon taya murna ga Amirul Hajji, tare da tabbatar da aniyar ma’aikatansa na yin aiki tare.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya naɗa Sarkin Dutse a matsayin Amirul Hajj domin jagorantar Alhazan jihar zuwa ƙasar Saudiyya a aikin Hajjin shekarar 2026.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
