Labarai
Jigawa: Hukumar Alhazai ta Tunatar da Maniyyata Game da Muhimmancin Biyan Kudin Hadaya
Daga Usman Muhammad Zaria
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa tayi kira ga maniyyatan da su himmatu don biyan kudin hadaya na aikin hajjin bana.
Darekta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka yayin taron bitar sanin makamar aiki ga ma’aikata tare da sabbin jami’an alhazai na kananan hukumomin jihar.

Yana mai cewar, biyan kudin hadayan cikin lokaci na naira 270 yana da muhimmaci domin cimma nasarar aikin.
Labbo ya kuma yi kira ga ma’aikatan hukumar da sabbin jami’an alhazai na kananan hukumomi 27 da su zamo masu tsoran Allah SWT yayin gudanar da aiyukan su gami da sauke nauyin da ya rataya a kansu a nan gida da kuma kasar Saudiyya.

Da ya waiwayi batun hakuri da maniyyata kuwa, Darakta Janar din yayi kira a gare su da su kasance masu hakuri tare da nuna juriya wajen tafiyar da al’amurran maniyyatan jihar.
Shi ma a nasa jawabin, Darektan tsare-tsare na hukumar, Alhaji Muhammad Garba ya ce akwai kwamitoci da dama da hukumar za ta kafa don cimma burin da aka sanya a gaba.


Ya kara da cewar, wajibi ne sabbin jami’an su rika halartar bita a cibiyoyin yankunansu domin fara sanin dukkan maniyyatan dake karkashin kulawar su.
Mohammad Garba, ya yi kira ga sabbin jami’an da su tabbatar da kula da lafiya da bada abinci da sa ido a masaukin Alhazai a Makkah da Madina da Arafat da mmMuna da sauran dukkan abubuwan da suka shafi Alhazai.

Babban limamin masallacin 744 dake Dutse kuma Sa’in Dutse, Malam Muhammad Yunusa yayi bayani mai tsawo kan muhimmacin aikin hajji.
Yana mai kara kira a gare su dasu maida hankali wajen halartar bita don sabawa da Alhazai tare da kara sanya ido akan mata kan yadda suke gudanar da aikin su a kasa mai tsarki.

Mahukunta hukumar sun gabatar da bayanai da dama kan ayyukan da suka shafi jami’an Alhazai da yadda ake dakile matsaloli idan bukatar hakan ta taso.
Daga bisani an baiwa sabbin jami’an kananan hukumomi 27 wato centre officers takardar nadin da aka yi masu na kula da walwala da jin dadin Alhazai.


Wasu daga cikin sabbin jami’an sun yabawa Gwamna Umar Namadi bisa nada su a matsayin jami’an kananan hukumomi tare da biya masu kudin hadaya.
Sun kuma jinjinawa Darekta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa karamcin da yake nuna masu wajen shirya taron sanin makamar aikin daya rataya a wuyansu.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
