Connect with us

Labarai

Jigawa: Hukumar Alhazai ta Tunatar da Maniyyata Game da Muhimmancin Biyan Kudin Hadaya

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa tayi kira ga maniyyatan da su himmatu don biyan kudin hadaya na aikin hajjin bana.

Darekta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka  yayin taron bitar sanin makamar aiki ga ma’aikata tare da sabbin jami’an alhazai na kananan hukumomin jihar.

Yana mai cewar, biyan kudin hadayan cikin lokaci na naira 270 yana da muhimmaci domin cimma nasarar aikin.

Labbo ya kuma yi kira ga ma’aikatan hukumar da sabbin jami’an alhazai na kananan hukumomi 27 da su zamo masu tsoran Allah SWT yayin gudanar da aiyukan su gami da sauke nauyin da ya rataya a kansu a nan gida da kuma kasar Saudiyya.

Da ya waiwayi batun hakuri da maniyyata kuwa, Darakta Janar din yayi kira a gare su da su kasance masu hakuri tare da nuna juriya wajen tafiyar da al’amurran maniyyatan jihar.

Shi ma a nasa jawabin, Darektan tsare-tsare na hukumar, Alhaji Muhammad Garba ya ce akwai kwamitoci da dama da hukumar za ta kafa don cimma burin da aka sanya a gaba.

Ya kara da cewar, wajibi ne sabbin jami’an su rika halartar bita a cibiyoyin yankunansu domin fara sanin dukkan maniyyatan dake karkashin kulawar su.

Mohammad Garba, ya yi kira ga sabbin jami’an da su tabbatar da kula da lafiya da bada abinci da sa ido a masaukin Alhazai a Makkah da Madina da Arafat da mmMuna da sauran dukkan abubuwan da suka shafi Alhazai.

Babban limamin masallacin 744 dake Dutse kuma Sa’in Dutse, Malam Muhammad Yunusa yayi bayani mai tsawo kan muhimmacin aikin hajji.

Yana mai kara kira a gare su dasu maida hankali wajen halartar bita don sabawa da Alhazai tare da kara sanya ido akan mata kan yadda suke gudanar da aikin su a kasa mai tsarki.

Mahukunta hukumar sun gabatar da bayanai da dama kan ayyukan da suka shafi jami’an Alhazai da yadda ake dakile matsaloli idan bukatar hakan ta taso.

Daga bisani an baiwa sabbin jami’an kananan hukumomi 27 wato centre officers takardar nadin da aka yi masu na kula da walwala da jin dadin Alhazai.

Wasu daga cikin sabbin jami’an sun yabawa Gwamna Umar Namadi bisa nada su a matsayin jami’an kananan hukumomi tare da biya masu kudin  hadaya.

Sun kuma jinjinawa Darekta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa karamcin da yake nuna masu wajen shirya taron sanin makamar aikin daya rataya a wuyansu.

 

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara