Labarai
Isra’ila Ta Kashe Kananan Yara Masu Dibar Ruwa A Gaza
Hukumar bayar da agajin gaggawa a Gaza ta ce aƙalla mutum 10, ciki har da ƙananan yara guda shida ne suka rasu a sanadiyar harin da Isra’ila ta kai ta sama a Gaza a safiyar Lahadi.
An kai gawarwakin waɗanda suka rasu zuwa asibitin Nuseirat’s al-Awda, inda wani likita ya ƙara da cewa sun yi jinyar wasu mutum 16, ciki har da ƙananan yara guda bakwai.
Wani ganau ya ce jirgi mara matuƙi ne ya harba makami mai linzami a kan dandazon mutanen da suka yi layi riƙe da jarkunansu domin ɗibar ruwa daga wata tankar ruwa a sansanin ƴangudun hijira na al-Nuseirat.
Har zuwa haɗa wannan rahoton, rundunar tsaron Isra’ila ba ta ce komai ba kan batun.
Wani faifan bidiyo da BBC ba ta tantance ba ya nuna ƙananan yara jina-jina, da gawarwakin wasu, wasu kuma suna ta ihu, sannan wasu suka zo daga bisani suna kwashe mutanen zuwa asibiti a motoci da amalanke.
Isra’ila ta fara kai hare-hare ne a Gaza tun bayan harin Hamas a ƙasar a ranar 7 ga Oktoban 2023, inda ƴan Hamas ɗin suka kashe 1,200, sannan suka yi garkuwa da wasu 251.
Zuwa yanzu Isra’ila ta kashe aƙalla mutum 57,882 a Gaza, kamar yadda ma’aikatar lafiyar yanki ta bayyana.
Haka kuma an tarwatsa sama da kashi 90 na gidajen zirin, sannan an lalata asibitoci da cibiyoyin ruwan sha da sauran abubuwan more rayuwa, wanda hakan ye jefa yankin cikin ƙarancin abinci da magani da man fetur.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
