Connect with us

Labarai

Hukumar Kwastam Ta Inganta Shirye-shiryen AfCFTA Kafin Taron Abuja

Published

on

Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ce tana ƙara ƙoƙari wajen aiwatar da cikakken tsarin Yarjejeniyar Cinikayya ta Nahiyar Afrika (AfCFTA), yayin da kasar ke shirin karɓar babban taron cinikayyar nahiyar a Abuja.

Babban Kwanturolan Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi, ya bayyana haka yayin da yake wa manema labarai jawabi a Fadar Shugaban Kasa kan shirye-shiryen Hukumar na karɓar taron Partnerships for African Customs and Trade (PACT).

Gwamnatin yanzu ta bayyana a fili cewa za ta yi amfani da cinikayya wajen inganta tattalin arziki da rage talauci.

Babban Kwanturolan ya kara da cewa sabon wa’adin da Shugaba ya ba shi ya ƙunshi aiwatar da Yarjejeniyar Cinikayya ta Nahiyar Afrika a matsayin muhimmin ma’aunin ayyukansa.

Ya ce manufar gwamnati ta haɗa da rage cunkoson tashoshin jiragen ruwa, zuba jari a muhimman kayan aikin tashoshi, da kuma amfani da sabbin fasahohi irin su single window domin saukaka cinikayya.

Shugaban Kwastam ya bayyana cewa ya gudanar da muhimman tattaunawa da shugabannin kwastam daga kasashen Afrika da ma’aikatar AfCFTA domin tabbatar da cewa hukumomin kwastam sun shiga tsakani sosai a tattaunawar aiwatar da yarjejeniyar.

Ya jaddada cewa kwastam na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da ka’idojin asalin kaya, bayar da rangwamen haraji, da kuma rage kudaden kwastam a hankali har su zuwa sifili tsakanin kasashen Afrika.

Adeniyi ya kuma bayyana kalubalen da ake fuskanta a shirin haɗin gwiwar tattalin arzikin yankin ECOWAS, musamman a tsarin ECOWAS Trade Liberalization Scheme, inda kasashe da dama suka kasa cika ka’idoji.

Ya ce wannan ne ya sa ake ƙara zurfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin kwastam, masu gudanar da harkokin kasuwanci, da sauran hukumomin da ke da alhakin kula da cinikayyar ketare.

Yayin da aka nada Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin Jagoran Cinikayyar Cikin Nahiyar Afrika, kuma Najeriya aka zaɓa ta karɓi baje kolin cinikayyar cikin nahiyar na gaba (Intra-African Trade Fair), Adeniyi ya ce hukumomi da dama irin su Hukumar Ƙarfafa Fitar da Kaya ta Najeriya (NEPC) da NEXIM Bank suna aiki tare wajen karkatar da kasuwancin Najeriya zuwa kasashen Afrika.

Ya tabbatar da cewa kasashen kwastam fiye da 30 daga Afrika sun yi rijista domin halartar taron, da yawancin su a matakin Darakta Janar. Kamfanoni masu zaman kansu—ciki har da masu jigilar kayayyaki, kamfanonin jiragen sama, masana’antu, da kamfanonin sufuri—su ne mafi rinjaye a cikin mahalarta.

Adeniyi ya ce za a fara taron ne da zaman musamman tare da ‘yan kasuwa masu zaman kansu domin jin kai tsaye matsalolin da suke fuskanta, ciki har da shingayen da ba na haraji ba (non-tariff barriers) da ke kawo tsaiko a cinikayyar nahiyar.

A kan batun kudaden shiga, Babban Kwanturolan ya ce ko da yake haraji na da muhimmanci, Hukumar ta karfafa sauran nauyin aikinta—tsaron kasa da saukaka cinikayya—ta hanyar amfani da sabbin kayan aiki da tsarin zamani. Wadannan abubuwa, a cewarsa, sun taimaka wajen kama muggan miyagun ƙwayoyi, makamai, da harsasai, tare da ƙaruwa sosai a kudaden shiga: kashi 70 cikin ɗari a shekarar 2023 da kuma kashi 101 cikin ɗari a 2024.

Ya kara da cewa Hukumar ta kusa sake zarce nasarorin kudaden shiga na shekarar 2025.

 

BELLO WAKILI 

Labarai

Labarai39 minutes ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai20 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara