Connect with us

Kasuwanci

Hukumar Kwastam Shiyar Jihar Kebbi Ta Sake Bude Kan Iyakar Najeriya Da Nijar

Published

on

 

Sabon Shugaban Hukumar Kwastam a Jihar Kebbi, Kwanturola Iheanacho Ernest Ojike, ya bi umarnin Shugaban Hukumar na kasa Bashir Adewale Adeniyi, na sake bude kan iyakar Kamba don ci gaba da hada-hadar kasuwanci a kasashen duniya.

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Mohammed Tajuddeen Salisu ya fitar, ya ce Kamba babbar kan iyaka ce mai matukar mahimmanci, da ke samar da kudaden shiga a jihar Kebbi.

Sanarwar ta bayyana cewa, sake bude kan iyakokin zai kara fadada kasuwanci ta halastacciyar hanya da za su yi tasiri wajen gina kasa da inganta tattalin arziki, yana mai cewa hakan ba ya nufin cewa za a yi sakaci ta yadda wasu za su yi amfani da wannan damar wajen shigo da haramtattun kayayyaki da za su yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa da kuma kawo cikas ga tsaron kasa ba.

Kwanturolan na jihar ya ce, jami’an hukumar a shirye suke don yin aiki bisa tsarin doka domin saukaka kasuwanci a kan iyakar Kamba ba tare da wata matsala ba, muddin ‘yan kasuwa sun shigo da halastattun kayayyaki da kuma biyan kudaden da suka dace ga asusun Gwamnatin Tarayya.

Sanarwar ta bayyana cewa, Kwanturola Ernest Ojike yana mai jaddada cewa, har yanzu an haramta fitar da kayan abinci zuwa kasashen waje, bisa la’akari da karancin abinci a kasar.

 

Abdullahi Tukur 

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara