Labarai
Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Samar Da Masauki Na Alfarma Ga Alhazan Jihar
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ta samar wa Alhazan Jiha katafaren masauki na alfarma a kusa da Harami da ke Makkah.
Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga wakilin gidan rediyon Najeriya a Dutse babban birnin jihar.
Ya ce hukumar ta samar da masauki na alfarma kusa da masallacin Harami, domin baiwa Alhazan jihar damar ziyartar babban masallacin ba tare da wahala ba.
Ya kuma bayyana cewa, Gwamna Umar Namadi a shirye yake ya ba hukumar tallafin da ya dace domin tabbatar da ganin Alhazan jihar sun yi ibada cikin sauki.
Dangane da ciyarwar kuwa, Labbo ya bayyana cewa, hukumar ta kulla yarjejeniya da wani kamfani don ciyar da Alhazan jihar jigawa a kasar Saudiyya.
Ya ce, hukumar na da kwarin gwiwar cewa kamfanin zai cimma yarjejeniyar ciyar da abincin yadda ya dace.
Shugaban ya yi nuni da cewa, mahajjatan da ke fama da rashin lafiya, wadanda ba za su iya cin abincin da aka tanadarwa Alhazai ba, za a basu kulawa ta musamman wajen samar musu da abincin da ya dace da lafiyarsu.
Ya yi nuni da cewa, hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta kayyade sama da naira miliyan takwas da dubu dari hudu (N8,457,685,59) a matsayin kudin aikin hajjin na bana.
Don haka ya yi kira ga maniyyatan da su kammala biyan kudadensu nan da ranar 30 ga watan Janairun, 2025.
Yayin da yake yaba wa ma’aikatan hukumar bisa jajircewa wajen gudanar da ayyukansu, ya umarce su da su kara zage dantse don ganin an samu nasarar aikin Hajjin na bana.
Labbo ya bayyana godiya ga gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Umar Namadi, da kuma hukumar alhazai ta kasa NAHCON bisa goyon bayan da suke baiwa hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa.#Hajj2025
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
