Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Samar Da Masauki Na Alfarma Ga Alhazan Jihar

Published

on

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ta samar wa Alhazan Jiha katafaren masauki na alfarma  a kusa da Harami da ke Makkah.

Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga wakilin gidan rediyon Najeriya a Dutse babban birnin jihar.

Ya ce hukumar ta samar da masauki na alfarma kusa da masallacin Harami, domin baiwa Alhazan jihar damar ziyartar babban masallacin ba tare da wahala ba.

Ya kuma bayyana cewa, Gwamna Umar Namadi a shirye yake ya ba hukumar tallafin da ya dace domin tabbatar da ganin Alhazan jihar sun yi ibada cikin sauki.

Dangane da ciyarwar kuwa, Labbo ya bayyana cewa, hukumar ta kulla yarjejeniya da wani kamfani don ciyar da Alhazan jihar jigawa a kasar Saudiyya.

Ya ce, hukumar na da kwarin gwiwar cewa kamfanin zai cimma yarjejeniyar ciyar da abincin yadda ya dace.

Shugaban ya yi nuni da cewa,  mahajjatan da ke fama da rashin lafiya, wadanda ba za su iya cin abincin da aka tanadarwa Alhazai ba, za a basu kulawa ta musamman  wajen samar musu da abincin da ya dace da lafiyarsu.

Ya yi nuni da cewa, hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta kayyade sama da naira miliyan takwas da dubu dari hudu (N8,457,685,59) a matsayin kudin aikin hajjin na bana.

Don haka ya yi kira ga maniyyatan da su kammala biyan kudadensu nan da  ranar 30 ga watan Janairun, 2025.

Yayin da yake yaba wa ma’aikatan hukumar bisa jajircewa wajen gudanar da ayyukansu, ya umarce su da su kara zage dantse don ganin an samu nasarar aikin Hajjin na bana.

Labbo ya bayyana godiya ga gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Umar Namadi, da kuma hukumar alhazai ta kasa NAHCON bisa goyon bayan da suke baiwa hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa.#Hajj2025

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara