Connect with us

Labarai

Hajj 2026: Jigawa ta Horas da Jami’an Alhazai na Kananan Hukumomi

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta shirya taron horas da masu horaswa (Train-the-Trainer)  da suka fito daga ƙananan hukumomi 27 na jihar, domin shirya su kan yadda za su horas da maniyyatan jihar da ke shirin zuwa aikin Hajjin shekarar 2026.

Da yake jawabi a yayin taron  horaswar na yini guda ga masu wa’azin yayin aikin Hajji na ƙananan hukumomi, Darakta Janar na hukumar ya bayyana cewa, an zabo su ne daga kananan hukumomi 27 na jihar domin aikin Hajjin da ke tafe.

Ya ce, waɗannan jami’an za su koma su horas da maniyyatan da ke shirin tafiya a cibiyoyin da aka tanada a ƙananan hukumominsu daban-daban a faɗin jihar.

Ya bayyana cewa, an shirya taron ne domin wayar da kan jami’an kan nauyin da gwamnatin jihar ta ɗora musu.

A cewarsa, an ɗauki wannan mataki ne domin tabbatar da samun ingantaccen horo ga maniyyatan jihar kan muhimman ginshiƙai da ka’idojin aikin Hajji.

Labbo ya jaddada cewa, samun ingantaccen ilimi ga maniyyata zai taimaka musu wajen gudanar da aikin Hajji bisa koyarwar addinin Musulunci tare da zama jakadu nagari ga jihar da ƙasa baki ɗaya.

Daraktan Janar ya ƙara da cewa, taron zai ba maniyyatan  damar sanin sahihanci da ingantattun ayyukan Hajji.

Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta raba jami’an zuwa kwamitoci daban-daban domin tabbatar da nasarar gudanar da ayyukan Hajjin shekarar 2026.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ƙara da cewa, a matsayinsu na jagororin maniyyata, wajibi ne su kasance kusa da maniyyatan domin ba su dukkan taimako da ake buƙata a Najeriya da kuma ƙasar Saudiyya.

Da yake tsokaci kan shirye-shiryen da ake yi, Daraktan Janar ya ce, hukumar ta riga ta karɓa tare da miƙa wasu daga cikin fasfofin ƙasashen waje na maniyyata domin samar da biza.

 

Ya yaba da yadda Gwamna Umar Namadi ya ɗauki nauyin kai masu horas da maniyyatan daga dukkan ƙananan hukumomi 27 na jihar zuwa ƙasar Saudiyya, yana mai bayyana hakan a matsayin abin a yaba.

Labbo ya shawarci mahalarta taron da su ji tsoron Allah wajen sauke nauyin da aka ɗora musu, yana mai cewa, hukumar ta samu gagarumar nasara a ayyukan Hajjin shekarar 2025.

Shugaban hukumar jin daɗin alhazai ya ce, Masarautar Saudiyya ta bai wa Jihar Jigawa lambobin yabo daban-daban, ciki har da kyallen da ake lullube Ka’aba da shi, wanda ake kira Kiswa, da sauran kyaututtuka, waɗanda dukkansu aka miƙa wa Gwamna Umar Namadi a fadar gwamnatin jihar da ke Dutse.

Tun da farko, Daraktan Wayar da Kai da Yaɗa Addini na hukumar, Alhaji Abdullahi Aliyu Hassan, ya yi jawabi ga jami’an kan nauyin da ke kansu a yayin ayyukan Hajjin shekarar 2026.

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, masana da dama sun gabatar da takardu a taron, ciki har da Dr. Abdulkadir Saleh Kazaure, Dr. Zakariyya Sa’idu Kandi, Malam Auwal Muhammad Ringim, Malam Isma’il Basirka da sauransu.

Wasu daga cikin mahalartan taron da suka yi magana da Rediyon Najeriya  sun yaba wa Darakta Janar na hukumar, Ahmed Umar Labbo, bisa shirya taron.

Sun kuma yi kira ga maniyyata da su ba da haɗin kai domin cimma manufofin da aka sanya a gaba.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara