Ilimi
Gwamnatin Neja Ta Rufe Makarantu Saboda Matsalar Tsaro
Daga Aliyu Lawal
Gwamnatin Jihar Neja ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun firamare da sakandare na gwamnati da na masu zaman kansu a fadin jihar sakamakon sace dalibai da aka yi a Makarantar St. Mary’s Catholic School da ke Papiri a Karamar Hukumar Agwara.
Gwamna Mohammed Umar Bago ne ya sanar da hakan a Minna bayan wata tattaunawar tsaro gaggawar ta da aka gudanar da shugabannin hukumomin tsaro, malaman addini da sauran masu ruwa da tsaki.
Ya ce matakin ya zama wajibi domin kare rayukan dalibai yayin da ake kara kokarin ceto yaran da aka sace.
Gwamna Bago ya jaddada cewa yanzu lokaci ne na daukar mataki a maimakon zargin juna, inda ya bayar da umarnin cewa a rufe dukkan makarantun mishan, da na Islamiyya da kuma kwalejojin gwamnati na tarayya har sai wani lokaci.
Haka kuma ya umurci a rufe dukkan manyan makarantu da ke yankin Neja ta Arewa da wasu yankuna masu hadari a Neja ta Gabas.
Gwamnan ya bukaci hukumomin tsaro, kungiyoyin fararen huhula, na kwadago da shugabannin addini su mayar da hankali wajen aikin ceto, yana mai tabbatar da kudirin gwamnati na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Yayin da yake bayyana lamarin a matsayin “abin bakin ciki da takaici,” Gwamna Bago ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da yin addu’a.
Ya ce har yanzu ba a tabbatar da yawan daliban Makarantar St. Mary’s Catholic School da aka sace ba, domin jami’an DSS, Rundunar ‘Yan Sanda da sauran hukumomin tsaro na kan aiki don tantance sahihin adadin daliban da abin ya shafa.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
