Labarai
Gwamnatin Kwara Ta Bada Tallafin Kayan Aikin Gona Ga Manoman Shinkafa
Akalla kungiyoyin manoman shinkafa talatin ne a karamar hukumar Edu ta jihar Kwara suka ci gajiyar shirin rabon kayan amfanin gona na gwamnatinjihar.
Kwamishinar noma da raya karkara ta jihar, Misis Oloruntoyosi Thomas ta bayyana haka a lokacin da take kula da rabon kayan amfanin gona ga kungiyoyi manoma a kauyukan Yelwa, da Bacita.
Ta yabawa Gwamnan jihar bisa namijin kokarin da ya yi na ganin an samu wadatar abinci a jihar.

Misis Thomas ta bayyana farin cikinta kan yadda aka samu nasarar rarraba kayayyakin a yankin.
Kwamishinar ta shawarci manoman da suka amfana da su tabbatar da yin amfani da kayan aikin gonan yadda ya kamata.
A nasa jawabin a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Shugaban kungiyar manoma ta Najeriya (AFAN) reshen jihar Kwara, Umar Mahmud-Aboki ya yabawa gwamnatin jihar kan yadda ta kai dauki ga manoma.
Tun da farko a nasa jawabin Etsu Tsaragi, Alhaji Aliyu Abdullahi wanda Santuraki na Tsaragi ya wakilta, Alhaji Jubril Gana -Jubril ya godewa gwamnatin jihar bisa aiwatar da shirin inganta rayuwar manoma.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
