Ilimi
Gwamnatin Kaduna Za Ta Mayarda Yara 200,000 Zuwa Makaranta
A wani yunkuri na rage adadin yara da suka daina zuwa makaranta, Gwamnatin Jihar Kaduna ta kaddamar da shiri mayarda yara 200,000 zuwa makaranta a cikin shekaru hudu masu zuwa, karkashin shirin Reaching Out-of-School Children (ROOSC).
An bayyana wannan shiri ne a wani taron bita na kwanaki biyu da aka shirya tare da haɗin gwiwar Save the Children.
A cewar, wakilin Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Salisu Baba Lawal shirin zai shafi dukkan ƙananan hukumomi 23 a faɗin jihar.
“Wannan shiri na Gwamnatin Jihar Kaduna ne tare da haɗin gwiwar abokan ci gaba da masu aiwatar da ayyuka,” in ji shi.
“Gwamnatin Jihar Kaduna ta samo lamunin tallafin kudi domin aiwatar da wannan shiri da nufin maganin matsalar yara da suka bar makaranta a faɗin jihar,” ya ƙara da cewa.
“Zuwo yanzu, an riga an horar da malamai 405, an gina sabbin makarantu 102, sannan ana ci gaba da gyara wasu makarantu 170.
Shirin yana ƙarfafa rajistar yara a makaranta da inganta koyarwa da samar da ingantaccen yanayi na koyo da koyarwa.”
Save the Children International da UNICEF su ne manyan abokan hulɗar wannan shiri, kuma yana samun goyon bayan kai tsaye daga Gwamna Uba Sani.
Save the Children ta raba kayan aiki da horar da malamai a karkashin shirin Reaching Out-of-School Children na Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Ma’aikatar Ilimi.
Shirin ROOSC yana mai da hankali kan ɗorewa, daidaito tsakanin jinsi, da kuma tallafawa marasa galihu, domin tabbatar da damar samun ingantacciyar ilimin firamare ga yara, matasa, da samari a fadin Jihar Kaduna.
Save the Children da UNICEF sun samu wakilci daga gwamnatin jihar ta hannun Ma’aikatar Ilimi don inganta tsarin koyarwa (Save the Children) da kuma ƙarfafa tsarin ilimi gaba ɗaya (UNICEF).
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
