Ilimi
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 3 Wajen Gina Azuzuwa A Makarantu
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana shirin ta na kashe sama da Naira biliyan 3 wajen gina sabbin azuzuwa a fadin kananan hukumomin jihar 44.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka a yayin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a gidan gwamnati dake Kano.
Ya ce gwamnati na da burin samar da yanayi mai kyau na koyo da koyarwa ta hanyar gina karin ajujuwa da gyara wadanda suka lalace.
Gwamnan ya bayyana cewa za a dauki sama da jami’an tsaro 17,000 aiki a fadin jihar domin tabbatar da tsaron kayayyakin makarantun firamare, inda za a tura mutum 400 a kowace karamar hukuma.
“Za a dauki masu gadi a yankunan da suke domin aiki a makarantun firamare da nufin tabbatar da ganin an kare makarantun yadda yakamata“.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ci gaba da cewa kowace karamar hukuma za ta samu Naira miliyan 25 domin gyara azuzuwa, inda hukumar kula da ilimin bai daya ta kasa za ta sa ido kan aikin domin tabbatar da ingancisa.
Ya kara da cewa zuba jarin ya nuna kudirin gwamnati na inganta ababen more rayuwa da samar da ingantaccen ilimi ga dalibai.
Abdullahi Jalaluddeen
-
Kasuwanci7 days ago
PDP Katsina Ta Zabi Sabbin Shugabanni
-
Labarai6 days ago
Kamfanin Mai Na Kasa Na Fuskantar Matsalolin Kudaden Samar Da Man Fetur
-
Labarai6 days ago
Gwamna Lawal Ya Yi Sabon Nadi Ga Hukumar Asusun Kula Da Harkokin Tsaro
-
Kasuwanci6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gina Rukunan Gidaje 500 A Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaba Bola Tinubu Ya Jajantawa Iyalan Yar’Adua Bisa Rasuwar Hajiya Dada
-
Labarai7 days ago
Ku Gaggauta Kammala Ayukkan Da Ke Hannun Ku A Arewa Maso Gabas
-
Labarai3 days ago
ACF Ta Ce Babban Kalubalen Arewa Yanzu Shi Ne Rashin Tsaro
-
Labarai6 days ago
APC Ta Lashe Dukkan Kujerun Kansiloli Da Kansiloli A Kebbi