Ilimi
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 3 Wajen Gina Azuzuwa A Makarantu
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana shirin ta na kashe sama da Naira biliyan 3 wajen gina sabbin azuzuwa a fadin kananan hukumomin jihar 44.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka a yayin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a gidan gwamnati dake Kano.
Ya ce gwamnati na da burin samar da yanayi mai kyau na koyo da koyarwa ta hanyar gina karin ajujuwa da gyara wadanda suka lalace.
Gwamnan ya bayyana cewa za a dauki sama da jami’an tsaro 17,000 aiki a fadin jihar domin tabbatar da tsaron kayayyakin makarantun firamare, inda za a tura mutum 400 a kowace karamar hukuma.
“Za a dauki masu gadi a yankunan da suke domin aiki a makarantun firamare da nufin tabbatar da ganin an kare makarantun yadda yakamata“.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ci gaba da cewa kowace karamar hukuma za ta samu Naira miliyan 25 domin gyara azuzuwa, inda hukumar kula da ilimin bai daya ta kasa za ta sa ido kan aikin domin tabbatar da ingancisa.
Ya kara da cewa zuba jarin ya nuna kudirin gwamnati na inganta ababen more rayuwa da samar da ingantaccen ilimi ga dalibai.
Abdullahi Jalaluddeen
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
