Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jihar Kaduna Za Ta Gina Sabbin Makarantun Sakandare 50 A Fadin Jihar

Published

on

Gwamnatin Jihar Kaduna ta kammala shirye-shiryen bayar da aikin gina makarantun sakandare 50 a fadin jihar.

Gwamnan jihar Malam Uba Sani ne ya sanar da hakan a lokacin da yake kaddamar da sabuwar babbar sakandare da aka gina a Rigachikun da ke karamar hukumar Igabi ta jihar.

Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa, makarantar  ta Rigachikun na daya daga cikin makarantun sakandire guda 62 da aka bada aikin gina su da kuma gyara a rukunin farko na shirin farfado da ilimi da  gwamnatinsa ta sanya a gaba.

A cewarsa, an kammala akasarin ayyukan da aka bada tare da kaddamar da su, yayin da ake gab da kammala sauran.

Uba Sani ya yi nuni da cewa, ko shakka babu sabuwar makarantar sakandaren za ta samar wa dalibai yanayin karatu mai kyau.

Idan za ku iya tunawa lokacin da na kaddamar da harsashin ginin wannan makaranta a ranar 31 ga watan Agustan 2023, na yi alkawarin cewa za a yi gaggawar kammala ta, yau gashi cikin ikon Allah  an cimma gacci”. Inji shi.

A cewarsa, hakan na nuni da gagarumin mataki a kokarin gwamnatinsa na magance daya daga cikin manyan matsalolin da ke kawo cikas ga fannin ilimi.

Hakazalika, Gwamnan ya kuma kai ziyarar gani da ido  cibiyar koyar da sana’o’i da ake ginawa a Rigachikun.

Aminu Dalhatu

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara