Connect with us

Labarai

Gwamnan Kano Ya Bada Umurnin Kama Duk Wanda Ya Fito Zanga-Zanga A Jihar

Published

on

Gwamna Yusuf ya haramta duk wata zanga-zanga a bainar jama’a, umarnin kama wasu dalibai da ake zargin sun yi zanga-zanga

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya takunkumi mai tsauri kan duk wani taron jama’a da aka yi niyyar gudanar da zanga-zanga a jihar, tare da yin amfani da ikon da aka bashi a matsayinsa na babban jami’in tsaro na jihar.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, kuma aka aikawa gidan rediyon Najeriya a Kano.

 

Sanarwar ta ce, bisa ga matsayinsa, gwamnan ya umarci ‘yan sanda, hukumar tsaro ta farin kaya, da hukumar tsaro ta Civil defense ta Najeriya da su kama, tsare, da gurfanar da duk wani mutum ko kungiyar da ke gudanar da zanga-zanga a kan titunan Kano. .

 

Wannan ƙwaƙƙwaran mataki dabara ce ta riga-kafi da nufin kawar da duk wata yuwuwar tabarbarewar doka da oda da maƙiyan jihar suka shirya.

 

“Muna samun sahihan bayanan sirri da ke nuni da cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar adawa a Kano sun tsara shirin daukar nauyin kungiyoyin dalibai da masu fafutukar siyasa daga wasu jihohin Arewa maso Yamma domin tada hargitsi a fake da cewa suna goyon bayan tsigaggen Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero. .”

 

Gwamnatin jihar ta fito karara ta haramta zanga-zanga ko jerin gwano ko wace iri ce, kuma za a kama mutanen da aka samu a kan titunan Kano suna yin irin wadannan ayyuka nan take.

 

“Ta wannan sanarwar, muna gargadin kungiyoyin dalibai da su guji yin amfani da masu tayar da kayar baya wadanda suka jajirce wajen tada rikici a Kano.”

 

Gwamnan ya bukaci daukacin al’ummar jihar da su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum domin jihar ta ci gaba da zaman lafiya, kuma gwamnati za ta ci gaba da sanya ido kan lamarin don gaggauta maganin duk wani mutum ko kungiyar da ke kokarin kawo cikas ga zaman lafiya da jihar ke samu a halin yanzu.

 

Saki/Abdullahi Jalaluddeen/Kano/Wababe

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara