Labarai
Gwamnan Jihar Kwara Ya Raba kudi Da Filaye Ga ‘Yan Wasan Jihar
Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya karbi bakuncin kungiyar kwallon kafa ta Kwara United bayan da suka zama zakaran gasar cin kofin shugaban kasa na 2025.
A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran Rafiu Ajakaye ya fitar ya ce gwamna AbdulRazaq ya kuma karbi bakuncin rukunin ‘yan kasa da shekara 19 na kungiyar da ta lashe gasar matasa ta kasa karo na farko.
Ta ce gwamnan ya bai wa kowanne dan wasan Kwara United kyautar naira miliyan biyar da fili a babbar karamar hukumar ta Kwara Smart City, inda ya yaba musu bisa yadda jihar ke alfahari.
Ta ce kungiyar ta Kwara United ta doke takwarorinta na Abakaliki FC a wasan da aka kamala da bugun daga kai sai mai tsaron gida bayan wasan na mintuna 90.
Tawagar ta yi nasarar shiga Ilorin ne a ranar Litinin da yamma, inda mazauna babban birnin jihar suka yi ta daga hannu da jinjina ga dogayen ayarin motocinsu daga Eiyenkorin zuwa dakin liyafar da ke gangarowar GRA inda aka gudanar da liyafar.
liyafar ta samu halartar manyan baki da dama ciki har da shugabar kwamitin majalisar dokokin jihar Kwara kan harkokin wasanni Hon Rukayat Shittu.END
REL/ALI MUHAMMAD RABIU
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
