Connect with us

Labarai

Gwamnan Jihar Kwara Ya Raba kudi Da Filaye Ga ‘Yan Wasan Jihar

Published

on

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya karbi bakuncin kungiyar kwallon kafa ta Kwara United bayan da suka zama zakaran gasar cin kofin shugaban kasa na 2025.

 

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran Rafiu Ajakaye ya fitar ya ce gwamna AbdulRazaq ya kuma karbi bakuncin rukunin ‘yan kasa da shekara 19 na kungiyar da ta lashe gasar matasa ta kasa karo na farko.

 

Ta ce gwamnan ya bai wa kowanne dan wasan Kwara United kyautar naira miliyan biyar da fili a babbar karamar hukumar ta Kwara Smart City, inda ya yaba musu bisa yadda jihar ke alfahari.

 

Ta ce kungiyar ta Kwara United ta doke takwarorinta na Abakaliki FC a wasan da aka kamala da bugun daga kai sai mai tsaron gida bayan wasan na mintuna 90.

 

Tawagar ta yi nasarar shiga Ilorin ne a ranar Litinin da yamma, inda mazauna babban birnin jihar suka yi ta daga hannu da jinjina ga dogayen ayarin motocinsu daga Eiyenkorin zuwa dakin liyafar da ke gangarowar GRA inda aka gudanar da liyafar.

 

liyafar ta samu halartar manyan baki da dama ciki har da shugabar kwamitin majalisar dokokin jihar Kwara kan harkokin wasanni Hon Rukayat Shittu.END

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara