Labarai
Gwamna Namadi Ya Bukaci Asibitin Koyarwa Na RSUTH Ya Bada Fifiko Ga ‘Yan Asalin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnatin jihar Jigawa ta yi kira ga hukumar gudanarwar asibitin koyarwa na Rasheed Shekoni da ta ba da kulawa ta musamman ga yan asalin jihar wajen daukar aiki.
Gwamna Umar Namadi ya yi wannan kiran a lokacin da babban likitan asibitin Dr. Salisu Mu’azu Babura da ma’aikatan asibitin suka kai masa ziyarar a gidan gwamnati dake Dutse.
Malam Umar Namadi ya bayyana cewar jihar Jigawa tana da kwararru da kuma masana da za su iya cike gibin guraben ayyukan lafiya a asibitin na Rasheed Shekoni.

Gwamnan ya kuma bada tabbacin ci gaba da tallafawa asibitin don cimma nasarorin da aka sanya a gaba.
Malam Umar Namadi ya kuma bayyana cewar gwamnatin jihar za ta kari fili domin yin karin gine gine a asibitin.
Tunda farko a nasa jawabin, Babban likitan asibitin Dr. Salisu Mu’azu Babura yace sun kai ziyarar ce domin gabatar da kansu da kuma neman karin hadin kai da goyan bayan gwamnatin jihar wajen ci gaban asibitin.

Dr. Salisu Babura ya shedawa Gwamnan ma’aikatan asibitin da gwamnatin tarayya ke biyan albashi sun kai 877.
Ya kuma yi nuni da cewar cikin adadin, guda 250 sun fito ne daga jihar jigawa.
Kazalika, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa hadin kai da goyan bayan da ke baiwa asibitin.

Yana mai fatan kara bullo da wasu hanyoyi domin magance kalubalen da ke fuskantar asibitin a yanzu.
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
