Connect with us

Labarai

EFCC Ta Cafke Manyan Motoci 21 Makare Da Kayan Abinci

Published

on

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta cafke manyan motoci 21 makare da kayan abinci da sauran kayayyaki, wadanda za a tsallaka da su kasashen Chadi, da Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya da kuma jamhuriyar Kamaru.

A wata sanarwa da jami’in yada labarai da hulda da jama’a na hukumar, Dele Oyewale, ya fitar, ya ce jami’an hukumar shiyar Maiduguri sun cafke manyan motocin a wani samame da suka kai a manyan hanyoyin fita da ke kan titin Gamboru Ngala da Bama a jihar Borno.

Sanarwar ta bayyana cewa, da farko ba a gano kayan abincin ba saboda yadda aka boye su cikin dubara a cikin manyan motocin, sai da jami’an suka zurfafa bincike.

Ya kara da cewa, binciken da aka yi ya nuna cewa, an shirya manyan motocin ne zuwa  N’djamena, da Jamhuriyar Chadi, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da kuma Kamaru, tare da lura da cewa, kamawar da aka yi za ta taimaka wajen dakile matsalar karancin abinci da masu fasa kwauri a fadin kasar ke haddasawa.

A cewar sanarwar, wadanda ake zargin a sun bayyana sunayensu kuma za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

Daga Dauda Iliya

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara