Kasuwanci
Bankin CBN ya Kayyade Yadda za a Rika Sayar da Dala
Babban Bankin Najeriya ya kayyade wa ’yan canji yadda za su rika sayar da Dala, da kuma ribar da za su dora.
A ranar Talata babban bankin ya sanar da hakan tare da cewa zai rika ba wa kowane dan canji mai rajista kudaden kasashen waje da kimarsu ta kai Dala N20,000 a kan kowace Dala, N1,301.
“Ribar da za su dora ba zai haura kashi daya cikin 100 na farashin da suka samu kudaden kasashen wajen daga hannun CBN ba,” in ji sanarwar mai dauke da sa hannun Daraktan Kasuwanci da Musayar Kudade na CBN, Hassan Mahmud.
Hakan na zuwa ne kimanin shekaru biyu da CBN, a karkashin jagorancin tsohon shugabanta, Godwin Emefiele, ya dakatar da ba wa ’yan caji kudaden kasar wajen.
Amma sabuwar sanarwar ta ce bankin ya lura tsohon tsarin ya haifar da tazara mai yawa a farashin Dala a hukumance da kuma a wurin ’yan canji.
A cewar sanarar, ana sa ran sabon matakin ba wa ’yan canji Dala zai hana tashin gwauron zabon da take yi da kuma rage bambancin tsakanin farashin gwamnati da na ’yan canji.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
