Connect with us

Labarai

An Kashe Wata Mata Bisa Kuskure A Jihar Kwara.

Published

on

Wasu fusatattun mutane sun kashe wata mata da aka yi kuskure daukar ta cikin masu garkuwa da mutane ce a babbar kasuwar Ipata da ke karamar hukumar Ilorin ta Gabas a jihar Kwara.

 

Gidan rediyon Najeriya ya tattaro cewa lamarin ya faru ne da safiyar alhamis, inda aka ga matar wadda daga baya aka gano ashe mai bukata ta musamman ce tana yawo a cikin al’umma.

 

Da yake tabbatar da lamarin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan (PPRO), Toun Ejire-Adeyemi, a wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.

 

“Bayanan sun samu cewa an ga wata mata da ake zargin wacce mai bukata ta musamman ce tana yawo a cikin al’umma, wasu jama’a da ba su sani ba sun yi zargin cewa ita ce mai garkuwa da mutane.

 

Ya kara da cewa, da gaggawa tawagar ‘yan sanda da ke sintiri suka garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka kubutar da matar da abin ya faru akanta sannan suka garzaya da ita babban asibitin Ilorin domin samun kulawar gaggawa.

 

Ya ce abin takaici, likitan da ya duba ta ya tabbatar da mutuwar ta sakamakon raunukan da ta samu.

 

Sanarwar ta ce an ajiye gawarwakinta a dakin ajiyar gawarwaki na asibitin, yayin da aka fara bincike mai zurfi.

 

ALI MUHAMMAD RABIU

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara