Labarai
An Kashe Wata Mata Bisa Kuskure A Jihar Kwara.
Wasu fusatattun mutane sun kashe wata mata da aka yi kuskure daukar ta cikin masu garkuwa da mutane ce a babbar kasuwar Ipata da ke karamar hukumar Ilorin ta Gabas a jihar Kwara.
Gidan rediyon Najeriya ya tattaro cewa lamarin ya faru ne da safiyar alhamis, inda aka ga matar wadda daga baya aka gano ashe mai bukata ta musamman ce tana yawo a cikin al’umma.
Da yake tabbatar da lamarin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan (PPRO), Toun Ejire-Adeyemi, a wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.
“Bayanan sun samu cewa an ga wata mata da ake zargin wacce mai bukata ta musamman ce tana yawo a cikin al’umma, wasu jama’a da ba su sani ba sun yi zargin cewa ita ce mai garkuwa da mutane.
Ya kara da cewa, da gaggawa tawagar ‘yan sanda da ke sintiri suka garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka kubutar da matar da abin ya faru akanta sannan suka garzaya da ita babban asibitin Ilorin domin samun kulawar gaggawa.
Ya ce abin takaici, likitan da ya duba ta ya tabbatar da mutuwar ta sakamakon raunukan da ta samu.
Sanarwar ta ce an ajiye gawarwakinta a dakin ajiyar gawarwaki na asibitin, yayin da aka fara bincike mai zurfi.
ALI MUHAMMAD RABIU
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
