Labarai
An jikkata Yan jarida bakwai a wani hari a Gaza

Akalla ƴan jarida bakwai ne suka jikkata sakamakon hari ta sama da Isra’ila ta kai asibiti a tsakiyar Gaza.
Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta kai wa cibiyar bayar da umarni ta masu ikirarin jihadi da ke harabar asibitin al-Aqsa hari, inda ɗaruruwan mutane ke fake wa.
Mutane huɗu sun rasa rayukansu, ciki har da wani mutum guda da Isra’ila ta bayyana a matsayin kwamandan mayakan Jihadi.
A wani sabon labarin kuma, sojin Isra’ilan sun baje kolin makaman da suka ce sojojinsu sun kama a wani samame da suka kai asibitin al-Shifa da ke birnin Gaza, bayan zargin mayakan Hamas da ɓuya a cibiyoyin lafiya.
Jami’an lafiya a Falasɗinu sun ce mutane tara ne suka rasa rayukansu a harin da Isra’ila ta kai a Bani Suhaila da ke makwabtaka da Khan younis.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
