Connect with us

Labarai

An Gina Riyojin Burtsatse ga yankunan da aka kai hari a Jihar Plateau

Published

on

Asusun tallafaws wadanda wata masifa ta fadawa ya gina riyojin burtsatse ga wasu al’ummomi da rikicin baya bayan nan ya Shafa a jihar Plateau.

Mai bada shawara na musamman ga shugaban asusun Janar Theophilus Danjuma, Mrs Toyosi Akenrele-Ogunsiji tace asusun na da manufar yaye wahalhalun da ‘yan Nijeriya suke sha.

Wakilinmu Josiah Buzun na dauke da karin bayani daga Jos.

Hare haren da aka rika kaiwa wasu kananan hukumomin jihar Plateau yayi sanadiyar jama’a da dama suka rasa kayyakin more rayuwarsu.

Wannan ne dalilin da ya sa asusun tallafawa wadanda masifa ta Shafa karlashin jagorancin Janar Theophilus Danjuma ya tona riyojin burtsatse don samarda ruwan sha ga al’umma.

An gina wadannan riyojin masu aiki da hasken Rana ga al’ummomin Doruwa, Babuje da Gassa a karamar hukumar Barikin Ladi, Sai Kuma a Ariri dake karamar hukumar Bassa da Kuma al’ummomin Sop dake tsalleken dogo a karamar hukunar Riyom.

Mrs. Akenrele Ogunsiji da ta wakilci shugabar asusun wajen bude wadannan ayukkan, tace mutane na bukatar tsaftaccen ruwan sha da wasu kayyayakin more rayuwa, don haka suke fara raba hatsi da Kuma kayan koyarwa da Kuma tallafawa don karfafa jama’a su dogara da kansu.

Mrs. Akenrele Ogunsiji tayi bayanin cewa, duk Wanda ke musu aiki da ya kasa gabatar da shi yanda ya dace zasu hukunta shi.

Shi kuma babbar daraktan asusun Farfesa Nana Tanko tace wajibi kowa ya amfana da wadannan riyojin da aka tona.

A jawabinsa babban sakataren hukumar bada agajin gaggauwa na jihar Plateau Mr. Sunday Abubu ya hori wadanda suka amfana da wannan aikin su kula da shi sosai.

Shugaban al’ummar Gassa da ke karamar hukunar Barikin Ladi James Toma ya godewa wannan asusun da shugabansa Janar Theophilus Danjuma saboda sanya farin cikin a tsakanin talakawan kasan Nan.

Wadanda suka amfana da shirin bayan yabon wannan asusun sun kuma bayyana imanin cewa wannan aikin zai taimaka wajen samar da ruwansha mai tsafta tare da kawarda cutuka da ake samu daga ruwa tare da fatan za a Sami Karin irin wannan aikin.

Josiah/Shafii Wababe

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara