Connect with us

Labaran Gida

An Bai Wa Kowanne Gwamna N30bn Ya Rage Tsadar Rayuwa A Jiharsa — Majalisar Dattawa

Published

on

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya ce Gwamnatin Tarayya ta bai wa kowanne gwamnan jiha naira biliyan 30 domin rage wa talakawa raɗaɗin tsadar rayuwar da suke fuskanta.

Akpabio ya bayyana haka ne a yayin zaman majalisar na ranar Talata, a ci gaba da tattauna irin halin ƙuncin da jama’ar kasar suka samu kansu a ciki, wanda ake dangantawa da cire tallafin mai.

Shugaban majalisar ya ce ya samu wadannan bayanai ne daga wajen Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji ta Kasa wadda ta miƙa wa jihohin waɗannan kuɗaɗen da ake magana a kansu.

Akpabio ya ce waɗannan kuɗaɗen daban ne da naira biliyan bib-biyu da aka bai wa gwamnonin a watan Satumbar bara daga cikin biliyan biyar-biyar na rancen samar wa jama’ar su tallafin rage raɗaɗin cire tallafin man fetur.

Shugaban majalisar ya bai wa gwamnonin shawara wajen yin amfani da waɗannan makudan kuɗaɗe ta hanyar da ta dace domin ganin jama’ar jihohin su sun samu tallafin da ya dace, musamman a bangaren abin da ya shafi abinci.

Akpabio ya ce ana iya cimma nasarar gabatar da tallafin ne ta hanyar amfani da shugabannin kananan hukumomi saboda kusancin su da mutanen da ke yankunan karkara.

Shugaban majalisar wanda ya yi Allah wadai da zanga-zangar da aka gani a wasu jihohin kasar da ake danganta su da tsadar rayuwa, ya zargi ‘yan adawa da daukar nauyin su, duk da kokarin da ya ce Majalisar Dattawan na yi domin tunkarar matsalar tare da Gwamnatin Tarayya.

Akpabio ya ce babu wani mahaifin da ke fatar ganin ɗansa ya kwanta ba tare da ya ci abinci ba, saboda haka ya buƙaci takwarorinsa da su mayar da hankali a kan ɗaukar matakin samo abinci duk inda yake domin wadata jama’a.

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara