Connect with us

Labarai

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Published

on

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon da ya gabata, sakamakon rashin bin umurninta na kaucewa kai hare hare a birnin Rafah dake kudancin Gaza.

Sakatare janar na Majalisar dinkin duniya Antoni Guterese ya ce babban kuskure ne mamayar da israila ta kai Rafah, la’akari da cewa an kasa amfani da hanyoyin da aka saba bi wajen isar da kayakin agaji, haka ma tuni aka rufe hanyoyi 2 mafi sauki da a ke bi dan shigar da kayayyaki cikin Gaza.

A jiya Talata ne rahotanni suka bayyana cewa bangarorin da ke rikici da juna sun amince da komawa kan teburin sulhu, domin tattauna batun tsagaita wuta tare da kawo karshen yakin na Israila da Hamas.

Rundunar sojin Israila ta ce tun da sanyin safiyar ranar Talata ne dakarunta suka kwace ikon kan iyakar mashigin Rafah bayan hare haren sama da suka shafe tsawon lokaci suna yi, wanda yayi sanadiyar mutuwar akalla mutane 27.

Ita ma Hukumar kare hakkin dan Adam ta Human Rights Watch, ta ce a kowace rana Falasdinawa da dama na fuskantar barazanar rasa rayukansu saboda hana kayayyakin agaji shiga inda suke da Israila ta yi.

Akalla Falasdinawa dubu talatin da hudu da  dari bakwai da tamanin da tara ne sojojin Israila suka kashe tun bayan barkewar yaki a cikin watan Oktoban shekarar 2023 yayin da wasu dubu saba’in da takwas da dari biyu da hudu suka jikkata.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara